‏إظهار الرسائل ذات التسميات JAN HANKALI. إظهار كافة الرسائل
‏إظهار الرسائل ذات التسميات JAN HANKALI. إظهار كافة الرسائل

الأحد، 23 ديسمبر 2018

ILLAR TALLACE TALLACE GA 'YA'YA MATA PART 2

ILLAR TALLACE TALLACE GA 'YA'YA MATA PART 2

Nawa aka kasa mata? Nawa ta kawo? Yaushe ta dawo? Wadansu za a ga suna tallar nono ko gyada ko fura ko mangwaro ko goro. Idan ka dauki jarin wata bai wuce Naira 500 ba, kuma sai ta kai kudin gida, ba tare da ta sayar da hajar ba! Sannan a wasu unguwanni akan ja irin wadannan ’yan mata zuwa gidajen maza, a yi musu fyade, ko a rika yi musu ciniki a inda ake gine-gine, inda kowane magini sai ya zagaya. Ko ka gan su a gidajen burodi ko tasha ko kasuwa suna bi rumfa-rumfa ko shaguna suna kai abinci!

Sannan a wasu lokuta akan yi abota da su a gidaje masu alfarma, ta  yadda za a yi wa wata madigo sannan a ba ta kudin kayanta, jin dadin haka sai ta rika zuwa yau da gobe abu ya zama jiki, daga nan sai ta kai bala’in kauyensu, inda abin da ake gani a birni ke bulla a kauye. A nan za a ci gaba da tsegumi, tsugunne ba ta kare ba.

 
Ina malamai, shin idan an yi karatun, an yi aiki da shi? Kuma a nan wane mataki gwamnati ta dauka wajen ganin  kowace yarinya ta yi karatu har zuwa akalla matakin sakandare?

A nan ma sai mutum ya rasa mene ne aikin kungiyoyin mata da masu rajin kare hakkokin bil-Adama da suke kau da kai kan irin wadannnan munanan dabi’u.

 
An san uba na da damar aurar da ’yarsa, amma ai ’yan uwa da malamai musamman makwabta na iya ba da shawarar a bari har sai ta yi kwari, musamman gudun cuttutuka kamar ciwon yoyon fitsari, ga masifa talauci da kyashi, domin wata tsananin talaucin kan sa ta fita daga kamanninta ta yadda ba wanda zai neme ta, har ta mutu a zawarci.

Sai an sa ido kan yadda mata, musamman dalibai ko mata ’ya’yan talakawa ko wadanda talauci ya daidaita suke tafiyar da rayuwarsu, domin bayanai sun tabbatar da cewa akan yi amfani da damar wajen keta mutuncinsu idan suna neman wasu bukatu a wajen maza a makarantu ko a kungiyance, balle masu zuwa gidajen aikatau a birane ko masu tsallakawa kasashen ketare don ci-rani.

Mafita tana ga gwamnati da malamai. Dole gwamnati ta tsaurara dokoki, musamman kan zamantakewa ta yadda za a rika ba da ingantaccen ilimi kyauta kuma a wajabta ga ’ya mace har zuwa sakandare. A ba masu hazaka sukolashif don zurfafa karatu a cikin gida da waje. Sannan malamai su shiga gaba wajen ba iyaye shawara da kan yadda za a tarbiyyantar da yara da neman aure da yadda zaman auren zai yi armashi.

Source. Jaridar Aminiya

ILLAR TALLACE TALLACE GA 'YA'YA MATA

ILLAR TALLACE TALLACE GA 'YA'YA MATA

Kusan ya zama ruwan dare ’yan mata su rika talla a birane da kauyukan kasar nan, musamman Arewa, duk da manazarta da dama na ganin wannan zamanin ya wuce. Ana maganar zamanin da ake shirin sarrafawa daga zaune, domin kullum duniyar dunkulewa take yi a waje daya.

Take hakkin ’ya mace ya wuce wai a lalata ta ko a yi mata fyade, domin sau da yawa ita ke kai kanta, kin ba ta damar cimma burinta shi ma take hakki ne. A kan haka ne wadansu kan yanke hukuncin cewa iyaye kan karfafa wa ’ya’yansu wajen zinace-zinace, da tu’amuli da miyagun kwayoyi da madigo, kai har hijira daga kasar, inda suke zama bakin haure, musamman idan mutum ya kalli yadda suke shiga ta yadda suke bayyana tsiraicinsu, har su rika yi maka tayi shin ba ka son abin da ka gani ne?

 
Bayan cinikin, su rika kiranka da maigida, yaya ko baba suna rangwada suna karya murya don su sace maka zuciya. Wadansu jagororin haya ake dauko su, sannan jagora na da kusanci da jagaliya, alaka da almajira, kuma su ne a kasa da talakawa a al’umma.

Da farko iyaye mata kan koya wa yara talla, yayin da yaran suka gane irin ribar da ake samu sai su guje wa makaranta, domin wadansu da sun dawo sun wurgar da jakar littattafan sai gobe da safe! Sannan kai kanka ka san wadansu jagororin mabaratan nan da biyu suke jansu, wadansu ma hayarsu ake yi, sai su caba ado, a bi tituna ana karbar na yau, kafin gobe wadansu suna aje magana! Musamman a duniyar da wayar salula kan taka rawar gani wajen haduwar sirri da mahada.

 
Wadansu iyayen kan nuna cewa da tallar yarinya za ta tara abin da za ka hada kayan daki, wai su ma tallar suka yi! Duk da cewa wadansu matasan kan samu horon kasuwanci daga tallar da suka yi lokacin kuruciya.

A haka wani zai samu jarin da zai kafa kansa har ya zama wani madugu.

Wani abin takaici da dama daga cikin masu tallar nan Musulmi ne, suna da iyaye ba marayu ba ne, abin tambaya a nan shin haka Musulunci ya umarce mu? Kuma kai me kake nema da har sai ’ya’yanka sun fita talla?

Wadansu daga safe har dare suna kan su kai karfe tara zuwa goma na dare kafin su nemi mai babur ya kai su kauyukansu! Ba boko ba Islamiyya, ana maganar karni na 21 inda ake tallar fura da nono ta kwanfuta, a yi ciniki da salula!

Wannan matsala ta talla ta haifar da matsaloli ga al’umma, kuma tana ci gaba da yada rashin kunya a tsakanin ’ya’ya da mahaifansu, sai kuma rashin ganin kimar malamai, dattijai da duk wani mai fada-a-ji a unguwa! Su ki karatu, sai gulma da kinibibi.

Irin wadannan matan da suke talla sun fi yiwuwar zama zaurawa, da dillalai ko kilakai masu zaman kansu. Tabbas ilimi na kara wa ’ya mace daraja da kima a kasuwar mata.

Za mu ci gaba

Source Jaridar Aminiya