Alkalin zaben, Idris Yunusa, yayin bayyana wannan sanarwa ya zayyana yadda shugaba Buhari dan takara na jam'iyyar APC ya lashe kuri'u 228 yayin da Atiku na jam'iyyar PDP ya samu kuri'u 138 a rumfar zabe ta 10 dake unguwar Mbamoi.
Kamar yadda kamfanin dillancin labarai na kasa ya ruwaito, baya ga samun nasara a mazabar sa ta Sarkin Yara da ke garin Daura a jihar Katsina, shugaban kasa Buhari ya kuma lallasa Atiku a mazabar sa ta unguwar Ajiya da ke birnin Yola.
0 Comments:
إرسال تعليق