الأحد، 24 فبراير 2019




Sule Lamido Ya Fita Kunyar PDP Da Atiku a Mazabar Sa A Zaben 2019

Home Sule Lamido Ya Fita Kunyar PDP Da Atiku a Mazabar Sa A Zaben 2019

غير معرف

Ku Tura A Social Media
A jiya, Asabar, 23 ga watan Fabarairu ne aka gudanar da zaben shugaban kasa da 'yan majlisar tayya ('yan majalisar wakilai da dattijai) a fadin kasar nan.
Tun a jiyan sakamako su ka fara fitowa daga mazabu daban-daban da ke fadin kasar nan. Sai dai har yanzu hukumar zabe ta kasa (INEC) ba ta fara fitar da sakamako a hukumance ba.
Zaben dai ya fi jan hankali ne a matakin kujerar shugaban kasa tsakanin manyn ‘yan takara; shugaba Buhari a jam’iyyar APC da babban abokin hamayyar sa, Atiku Abubakar, dan takarar jam’iyyar PDP.
Manema labarai da ‘yan jarida sun fi mayar da hankali a kan sakamakon mazabun manyan ‘yan siyasa da ke goyon bayan ‘yan takarar biyu.
Wata majiyar mu daga jihar Jigawa ta sanar da mu cewar tsohon gwamnan jihar, Alhaji Sule Lamido, ya fita kunyar jam’iyyar PDP da dukkan ‘yan takarar ta na kujerar shugaban kasa da na majalisar tarraya.
Tsohon gwamnan ya kada kuri’ar sa a mazabar sa ta Bamaina ‘C’ da ke garin Bamaina a karamar hukumar Birnin Kudu.
A matakin kujerar shugaban kasa jam’iyyar PDP ta samu kuri’u 259 yayin da APC ta samu kuri’u 20.
Jam’iyyar PDP ta samu kuri’u 278 a zaben kujerr dan takara Sanata yayin da APC ta samu 6. A matakin kujerar majalisar wakilai PDP ta samu kuri’u 267 yayin da APC ta samu 17.

Share this


Author: verified_user

0 Comments: