Showing posts with label Labari da Dumi-Dumin Sa. Show all posts
Showing posts with label Labari da Dumi-Dumin Sa. Show all posts

Tuesday, 29 January 2019

KARANTA KAJI: YAZAMA DOLE MU SALLAMI GWAMNATIN BUHARI SABODA BABU ABINDA TA TSINANAWA 'YAN NIGERIA - ZAHARADDEN SANI

KARANTA KAJI: YAZAMA DOLE MU SALLAMI GWAMNATIN BUHARI SABODA BABU ABINDA TA TSINANAWA 'YAN NIGERIA - ZAHARADDEN SANI

Fitaccen Jarumin fina-finan Hausa Zaharaddeen Sani ya caccaki gwamnatin shugaba Buhari.



A cewar jarumin "Idan har munason ƙaruwar tattalin arziki, ci gaban ƙasar mu da makamantan su yazama dole mu marawa Atiku Abubakar baya a zaɓen 2019".

Kamar yadda wakilin Muryar Hausa24 ya shaida mana "Jarumin ya ƙara da cewa, A shekarar dubu biyu da tara (2019) muna da 'yan takara guda 2 kacal Atiku Abubakar shine ya dace da Nijeriya".

Kalli Cikakken bidiyon  yadda Jarumin yake caccakar gwamnatin Buhari tare da abokanan aikin sa (Jaruman Kannywood), bidiyon ya jawowa jarumin baƙin jini awajen masoyan sa.


DOWNLOAD VIDEO HERE


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: www.MuryarHausa24.com.ng

Saturday, 29 December 2018

KARANTA KAJI: TA RASU AWANNI KADAN SUKA RAGE MATA TA ZAMA AMARYA ALLAHU AKBAR!

KARANTA KAJI: TA RASU AWANNI KADAN SUKA RAGE MATA TA ZAMA AMARYA ALLAHU AKBAR!

Sunanta Fauziyya Abdulkadir Tataru, ta kammala karatunta a Makarantar ATBU Bauchi, ta gamu da Ajalinta a yayinda da ake Shagulgulan daurin aurenta a jiya Juma'a da misalin karfe 9:30pm, yayinda kuma daurin auren nata ya kasance yau Asabar ne da misalin karfe 11:00am.




Tana farin cikin za ta dakin miji ashe kabari za ta. Hausawa sun ce ana bikin duniya ake kiyama, da yammacin Jiya juma'a ne aka yi walimar auren ta, kwatsam sai ga shi cikin daren jiyan Allah ya dauki ran ta.


Fauziyya Abdulkadir Tataru, yarinya ce wanda za'a daura Aurenta a yau 29/12/2018 da misalin karfe 11:00am na safe a masallacin Gwallaga dake Bauchi Da Angonta Abduljalil Salisu Boyi.


Yau da safe ne ranar daurin auren ta a masallacin Gwallaga dake jahar Bauchi, sai ga shi yau din ne za ayi jana'izar ta. Allahu akbar!

Awanni kadan suka rage ta zama Amarya, Allah ya karbi rayuwarta.


Wannan shine abinda Muhammad Kabeer Bauchi Ya wallafa a shafin sa"Sunanta Fauziyya Abdulkadir Tataru, ta kammala karatunta a Makarantar ATBU Bauchi, ta gamu da Ajalinta a yayinda da ake Shagulgulan daurin aurenta a jiya Juma'a da misalin karfe 9:30pm, yayinda kuma daurin aurennata ya kasance yau Asabar ne da misalin karfe 11:00am."

Ayayinda nayi kokarin jin ta bakin wassu daga Makusantar Marigayiya Fauziyyan cewa ko tayi fama da rashin lafiya ne? Sun tabbatar mun da cewa, lallai tana cikin koshin lafiyarta a yayin shirin Biki, sai dai sun tabbatar mun da cewa, tun kafin daurin auren akwai wani tsohon Samarinta dan Maiduguri Wanda ya ce mata 'Ayi auren mana ya gani' tabbas wannan kalma nasa ta tayar wa al'umma da hankali.


Wannan shine abinda Muhammad Kabeer Bauchi ya shaidawa wakilin mu.

Allah buwayi gagara misali, mahaliccin da ya fi Angonta kaunarta ya dauke abinsa.

Allahu akbar! Ita da kanta ta rubuta sanarwar daurin auren ta a shafinta.


Allah ya jikan wannan baiwar Allah ya gafarta mata, da rahama, ya mata makoma da madaukakiyar aljanna firdausi Amin Summa Amin.


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: www.MuryarHausa24.com.ng


Friday, 28 December 2018

Karanta Kaji: Abubuwan da Yakamata Ku Sani game da Marigayi Shehu Shagari

Karanta Kaji: Abubuwan da Yakamata Ku Sani game da Marigayi Shehu Shagari

Bayanan da muka samu daga iyalan tsohon shugaban Najeriya Alhaji Shehu Usman Aliyu Shagari ya rasu ranar Juma'ar nan. Tshohon shugaban ya rasu ne a asibitin kasa da ke Abuja inda yake jinya.


Alhaji Shehu Shagari ya rasu yana da shekara 93 a duniya, bayan ya sha fama da jinya.
Ya shugabanci Najeriya daga 1979 zuwa 1983, lokacin da sojoji suka yi gwamnatinsa ta jamhuriya ta biyu juyin mulki, inda Janar Muhammadu Buhari ya zama shugaban kasa.
Alhaji Shehu Shagari yana cikin 'yan siyasar jamhuriya ta farko, da suka yi ministoci a gwamnatin Tafawa Balewa tsakanin 1960 zuwa 1966 da sojoji suka yi wa gwamnatin juyin mulki.
Ya rasu ya bar 'ya'ya 19, maza takwas mata 11 da jikoki da dama.
Gabanin rasuwarsa ya rike sarautar Turakin Sakkwato, wanda babban wakili ne a majalisar koli ta fadar Sarkin Musulmi.
Ya rike wannan sarauta tun daga 1962 har zuwa rasuwarsa.
An garzaya da shi zuwa asibiti a Abuja ne bayan da jikinsa ya yi tsanani a ranar Talata.
Alhaji Shehu Shagari ya sha fama da ciwon Limoniya.
Ana sa ran za a mayar da shi Sakkwato ranar Asabar domin yi masa jana'iza.

KARANTA KAJI: TAKAITACCEN TARIHIN ALH SHEHU SHAGARI



Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode


Wednesday, 26 December 2018

Karanta Kaji: 'Yan sandan Najeriya 190 sun tsere saboda tsoron yaki da Boko Haram

Karanta Kaji: 'Yan sandan Najeriya 190 sun tsere saboda tsoron yaki da Boko Haram

Rahotanni daga Najeriya na cewa, jami’an ‘yan sandan kasar 190 sun tsere daga horon da ake ba su na musamman a wata makarantar horas da sojoji da ke garin Buni Yadi na jihar Yobe a yankin arewa maso gabashin kasar.


Tserewar Jami'an na zuwa ne bayan wasu bayanai da ke nuna cewa, ana shirin tura su wuraren da ake kan ganiyar fama da rikicin Boko Haram da suka hada da kan iyakokin Chadi da Nijar.
Adadin dai wani bangare ne na 'yansanda dubu 2 da babban Sufeto Janar na ‘yan sandar kasar, Ibrahim Idris ya yi alkawarin bayarwa don taimakawa sojoji wajen yaki da mayakan Boko Haram.

Tuni dai shalkwatar 'Yan sandan ta yi umarnin kame mutanen 190 don fuskantar hukunci.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: RFI HAUSA

Wednesday, 19 December 2018

Karanta Kaji: Dalilin Da Yasa ‘Yan Majalisar Tarayya su Yiwa Buhari Ihun Bamayi Tare da Martanin da Buhari Ya Mayar Musu Mai Zafi

Karanta Kaji: Dalilin Da Yasa ‘Yan Majalisar Tarayya su Yiwa Buhari Ihun Bamayi Tare da Martanin da Buhari Ya Mayar Musu Mai Zafi

A cikin wani yanayin na ban-tausayi, Shugaba Muhammadu Buhari ya shawarci ‘yan Majalisar Tarayya da su daina tozarta Najeriya a lokacin da duk duniya ke kallon abin da ke gudana a zauren Majalisar.
Shugaba Buhari yayin gabatar da kasafin kuɗi na 2019


Hakan ya biyo bayan cin fuskar da Buhari ya fuskanta da kuma tozarta shi da wasu mambobi suka yi, a lokacin da ya ke gabatar da kasafin kudi na 2019.
An rika yi masa iho da sowa da furta ba ma yi, ba mayi. Wasu ma sun rika wuce gona da iri, su na cewa karya ce.
A cikin tattausar zuciya, shugaba Buhaeri ya roki mambobin da su daina abin da suke yi, domin duniya gaba daya na kallon abin da ke faruwa.
Buhari ya shaida musu cewa wannan ne kasafin kudi na karshe da zai gabatar wa majalisar a wannan zango na sa.
Ya dai sake tsayawa takarar shugabancin kasa a karo na biyu, wanda idan bai yi nasara ba, wannan ne zai kasance kasafi na karshe da ya gabatar a zauren majalisar.
A baya ya gabatar da na 2016, 2017, 2018 da kuma na yau, 2019.
MUN FUSKANCI KALUBALE A SHEKARU UKU BAYA
Buhari ya tabbatar musu da cewa a sheakaru uku da suka gabata, Najeriya ta fuskanci babban kalubale, amma kuma tattalin arzikin ya fita daga cikin halin kaka-ni-ka-yi da kasar nan ta tsinci kan ta.
Ya yarda da cewa wasu ayyukan ci gaban da aka kasa gudanarwa ya faru ne dalilin matsalar tsaro a cikin kasar nan.
ZA MU KAWAR DA MATSALOKIN BOKO HARAM DA RIKICIN MAKIYAYA DA FULANI
Duk da dai ya na magana ana karyata shi, Buhari bai daina furta inda kasar nan ta sa a gaba ba, har ya ci gaba da bayanain cewa an dauko hanyar magance matsalar makiyaya da kuma manoma da rikicin Boko Haram.
HALIN DA ASUSUN NAJERIYA KE CIKI
Shugaba Muhammadu Buahri ya shaida cewa a hanlin yanzu, lalitar Najeriya ta kasashen ketare adadin ta ya kai dala bilyan 42.92 ya zuwa cikin wannan wata na Disamba, 2018.
Ya ce amma a sheakaru uku baya cikin Mayu, 2016 adadin kudin da ke cikin lalitar bai zarce dala bilyan 20.57 ba.
MAIDA HANKALI GA KAMMALA MANYAN AYYUKAN RAYA KASA
Cikin jawabin Shugaba Buhari, ya yi mahganar cewa gwamnatin sa ta maida hankali sosai wajen kokarinn ganin an kammala manyan ayyukan da gwamnatin ta sa a gaba ba a kai ga kammalawa ba.
Ya kuma bugin kirjin cewa babu wata jiha a dukkan fadin kasar nan da ba a gudanar da wani gagarimin ayyukan gwamnatinn tarayya a cikinn ta.

Shugaba Buhari lokacin da yake gabatar da kasafin kuɗi na shekarar 2019



MATSAYIN KASAFIN 2018 DA YA GABATA
Buhari ya ce kasafin 2018 na shekarar da ya kamata, ya wuce amma ya bar kwantai din ayyuka. Ya ce daga cikin naira tiriliyan 9.2 da aka yin kasafi a shekarar 2018, naira tiriliyan 4.59 kacal aka kashe ya zuwa cikin watan Satumba, 208 da mun ke ciki.
Ya ce akwai ayyuka da kirdadon ragowar naira tiriliyan 6.84 da ba a kai ga cimma ba.
Sai dai kuma ya ce duk sauran kwantai din, an saka ayyukan a cikin kasafin 2019.
NA AMINCE DA KARIN ALBASHI
Shugaba Muahammadu Buhari ya shaida wa majalisa cewa ya amince da karin albashi wanda ake ta sa-toka-sa-katsi a kan sa.
Ya kuma ce nan ba da dadewa ba zai aiko da kudirin da ya ke so majalisa ta maida karin albashin ya zama doka. Sannan kuma zai kafa kwamitin da zai gano yadda za a rika samar wa karin albashin kudaden da za a rika tafiyar da tsarin.


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source:Premium Times Hauss

Friday, 23 November 2018

KARANTA KAJI: YADDA AKA FANSO 'YAN TAGWAYEN DA AKAYI GARKUWA DA SU A ZAMAFARA DA DARASIN DA ZAMU KOYA

KARANTA KAJI: YADDA AKA FANSO 'YAN TAGWAYEN DA AKAYI GARKUWA DA SU A ZAMAFARA DA DARASIN DA ZAMU KOYA

Lokacin da Maigirma Sanata Kabiru Marafa ya bada tallafinshi Naira miliyon shida da sauran kudin da jama'ar Nigeria suka tallafa aka hada kudin ya kai Naira miliyon goma sha biyar, sai aka kira wadanda sukayi garkuwa da tagwayen aka sanar musu cewa kudin ya cika kamar yadda sukace a biyasu kafin su saki tagwayen, bayan an sanar da su cewa kudin ya cika sai sukace to a jirasu zasu kira don a kai musu kudin.



Bayan kamar awa uku sai suka kira wayan Ibrahim mijin yayarsu wanda ake sasantawa da shi, sukace a dauko kudin azo wani gari da ake kira Gurbin-Burai inda kwanaki masu garkuwa da mutane sukayi kashe-kashe da kone-kone sukace idan an isa garin a kirasu, kafin su Ibrahim su isa garin masu garkuwa da tagwayen suna ta kiransu a waya cewa mai yasa har yanzu ba su iso ba? sun gaji da jira, su fa zasu kashe tagwayen suyi tafiyarsu sai dai azo a dauki gawarsu, Ibrahim dai yayi ta basu hakuri yana cewa mun kusan isowa.

Bayan su Ibrahim sun isa garin na Gurbin-Burai suka kira masu garkuwan aka fada musu cewa sun iso garin, sai sukace to daga nan su biyo ta wani kauye da ake kira Dumburum daga Dumburum daji za'a shiga, to su Ibrahim sai suka ajiye motarsu suka nemi mashina guda uku, sai masu garkuwan suka kira waya sukace ai mun ganku ko taho garin na Dumburum zamu fada muku hanyar da zakubi ta kawoku cikin jeji inda muke, jama'a kunga wannan ya nuna cewa akwai masu yiwa 'yan bindigar leken asiri ko ta ina a cikin wadannan garuruwa na Zamfara.

Daga garin Dumburum su Ibrahim sunyi tafiya kamar tsawon kilo mita 15 a cikin jeji, suna cikin tafiya kawai sai suka fara ganin mutane da bindigogi suna ta bullowa wanda yawansu ya kai kusan mutum dari da hamsin, kuma kowa rike yake da bindiga kirar AK47 ana cewa su dakata a gurin, sai su Ibrahim suka dakata suka sauka daga kan mashina, da ma su uku ne, da shi Ibrahim mijin yayarsu, da wanda zai auri Hussaina, da babban yayansu, sai Ibrahim ya dauko kudin ya ajiye a gabansa wanda aka zuba kudin a cikin jaka guda biyu, 'yan bindigar sun gewayesu a tsakiyar jeji, bayan kamar mintuna biyu sai ga shugaban kuma ogan 'yan bindigar ya bullo tare da tawagarsa rike da manyan bindigogi tagwayen suna bayanshi.

Haka shugaban barayin ya matso har kusa da Ibrahim inda kudin suke ajiye a cikin jaka a 'kasa, bai ce masa komai ba sai yayi umarni da wasu yaranshi guda biyu su bude jakan su kirga kudin, bayan sun kammala kirga kudin gaba daya ya cika miliyon 15, sai ogan yace a mayar da kudin cikin jaka a daure, da akayi haka, sai ogan barayin ya tsuguna a gaban kudin ya debi kasa da hannunshi ya watsa akan jakakkunan kudin, sai ya mike tsaye ya hau kan jakakkunan kudin da kafafunshi, sai ya daga kanshi sama yana karanta wasu 'dalasimai irin na tsafi, yana tayi har kusan kamar mintuna 2 sai ya saukar da kanshi kasa, ya kuma sauka daga jakar kudin ya ja da baya, sai yayi umarni ga yaranshi da su dauki kudin, sai suka dauka, sai ya kalli Ibrahim yayi dariya sai yace sannunku da zuwa ashe kuna son kannenku.

Sai Ibrahim ya amsa masa, sai yace ai ba wanda baya son kannenshi oga, daga nan sai yayi umarni da a kawo tagwayen ya mikasu ga Ibrahim yace su juya su tafi kar su kuskura su juya baya, Ibrahim yace mun gode oga, shine suka dauko tagwayen suka iso har kauyen Gurbin-Burai inda motarsu take, daga nan sai Ibrahim ya fara kiran waya suna sanar da 'yan uwa da wadanda suka tallafa cewa tagwayen sun kubuta lafiya.

Jama'a wannan shine bayanin abinda ya faru game da yadda akaje aka karbo tagwayen.

Abinda bincikenmu ya tabbatar mana shi ne an jima ana bibiyar tagwayen domin ayi garkuwa da su, mutane da dama suna da hannu a cikin garkuwa da 'yan matan, wato nazarin da mukayi a kai shine wadannan masu aikata laifin garkuwa da mutane sun kawo wata sabuwar hanyar yin garkuwa da mutane ta hanyar bibiyar mutanen da suke mu'amala da dandalin sada zumunta na zamani musamman wadanda suke watsa hotunansu a social media, masu garkuwan suna la'akari da farin jinin wanda yake social media da yawan jama'ar da suke tare da shi wanda idan sunyi garkuwa da shi dole za'a biyasu kudi.

Kunga wadannan tagwaye babban abinda yayi sanadiyyar jefa su cikin wannan bala'i shine saka hotunansu da suke yi a social media da irin yadda ake kambamasu, wadanda sukayi garkuwa da su sun dauki lokaci mai tsawo suna bin diddiginsu har zuwa ranar da tagwayen suka ziyarci garin Mahaifinsu domin su raba katin aurensu, garin kauye ne, a daren ranar da za'ayi garkuwa da su tun isarsu garin suke ta yawo, kuma duk inda suka wuce sai an nunasu, da dare yayi misalin karfe 11 da wasu mintuna akaje gidan kawarsu da suka sauka zasu kwana aka sacesu gaba daya, har da kanin mijin kawar tasu, da ita kawar tasu aka tafi dasu jeji.

Muna nazarin ayyukan masu garkuwa da mutane da dabarunsu, mun sani cewa idan masu garkuwa da mutane sun kama mutum biyu ko sama da haka, to ba sa yarda su sake daya ko biyu su bar wani, a'a sai dai su sakesu gaba daya, to amma wannan sun kamasu gaba daya, sai suka saki tagwayen sauran kuma ba'a sakesu ba, wannan zai tabbatar maka da cewa masu garkuwan sunyi karfin da ya wuce tunanin duk wani mai tunani ko hasashe da nazari, kuma wannan babban kalubale ne ga gwamnatin Nigeria, mahukunta sai sunyi da gaske imba haka ba masifar zata mamaye jihohi da dama a Nigeria.

Daga karshe ina kira ga 'yan mata da mazaje masu yada hotunansu a kafofin sada zumunta kuma suke da dunbin masoya da suyi taka tsantsan, sannan su kiyaye sirrin tsaron kawunansu, ku dena bayyana inda zakuje idan zakuyi tafiya, bayyanawan hatsari ne mai girma a irin wannan lokaci da muka tsinci kanmu, a dinga 6atar da kafa idan za'ayi tafiya ko za'a dawo daga tafiya.

Muna rokon Allah Ya tsaremu daga dukkan sharri da makirci da mugun tarko.

Yaa Allah duk masu bibiyarmu da sharri ko cutarwa Allah Ka mayar da sharrin da cutarwan zuwa kansu Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source:  Datti Assalafy



Tuesday, 20 November 2018

Karanta Kaji: Zan Fitar da Talakawa Miliyan 50 daga Kangin Talauci cikin Shekaru 2 - Atiku Abubakar

Karanta Kaji: Zan Fitar da Talakawa Miliyan 50 daga Kangin Talauci cikin Shekaru 2 - Atiku Abubakar

Ɗan takarar shugaban kasa karkashin jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar ya fara yakin neman zabenshi yau, Litinin ta shafinshi na sada zumunta inda ya fara da bayar da labarin cewa ya taso maraya kuma har sayar da itace yayi.



Yace ya sayar da itace a kan titunan garin Jada dake Adamawa amma Allah, ta sanadiyyar Najeriya ya daukakashi.

Yace idan Najeriya ta bashi irin wannan damar ya kai yanda yake a yanzu to shima yana da aikin gyara Najeriyar yanda zata baiwa kowane danta irin waccan dama.

Yayi kira ga 'yan Najeriya da su bishi akan wannan tafiya ta samar da rayuwa me kyau.

Yace idan aka zabeshi zai taimakawa kananan da matsakaitan masana'antu miliyan 50.

Yace wannan tsari zai samar da ayyuka miliyan 2.5 sannan cikin shekaru 2 mutane miliyan 50 zasu fita daga kangin talauci.

Yace kuma akwai wani tsari da zai fito dashi na horas da mata da maza miliyan daya duk shekara akan sana'o'i daban-daban.

Yace akan maganar shirinshi na canja fasalin Najeriya kuma zai samar da yanayin da jihohi da gwamnatin tarayya zasu samu kudin shiga fiye da da.

Ya kara da cewa ga wanda ke so ya karanta tsare-tsaren nashi zai iya yin haka a shafinshi na Atiku.org.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: Hutu Dole

Sunday, 18 November 2018

Karanta Kaji: An Sako Tagwayen Da 'Yan Bindiga Su Ka Sace a Zamfara

Karanta Kaji: An Sako Tagwayen Da 'Yan Bindiga Su Ka Sace a Zamfara

An sako tagwayen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su a jihar Zamfara, bayan da aka biya su kudin fansa.


Rahotanni daga jihar Zamfara a Najeriya na cewa da yammacin jiya Asabar masu garkuwa da mutane sun sako ‘yan matan nan tagwaye da suka sace tun watan jiya.

An sako Hasana da Usaina ne bayan da aka biya kudin fansa da adadinsu ya kai Naira Miliyan 15, da aka samu tarawa da taimakon wasu dai dai kun jama’a, harma da ‘yan siyasa a ciki da wajen jihar Zamfara.

Sai dai an sako tagwayen ne kadai ba tare da ‘yar uwarsu Sumaiya ba, wacce aka sace su tare a gidan aurenta a garin Dauren.


Wakilin Sashen Hausa na Muryar Amurka, Murtala Faruk Sanyinna ya zanta da daya daga cikin ‘yan uwan yaran, Abubakar Muhammad Zurmi.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: VOA HAUSA

Friday, 9 November 2018

Karanta Kaji Dalili: Gwamnati na kashe naira milyan 3.5 wajen ciyarwa da kula da El-Zakzaky – Lai Mohammed

Karanta Kaji Dalili: Gwamnati na kashe naira milyan 3.5 wajen ciyarwa da kula da El-Zakzaky – Lai Mohammed


Ministan Yada Labarai, Lai Mohammed ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya na kashe naira milyan 3.5 wajen ciyar shugaban mabiya Shi’a, Sheikh Ibrahim El-Zazaky, wanda ke tsare kusan shekaru uku kenan.


Ana tsare da El-Zakzaky tun cikin watan Disamba, 2015 bayan da sojoji suka kashe mabiyan sa kimanin 347.
An zargi mabiyan sa da tare hanya suka hana Hafsan Hafsoshin Kasar nan, Tukur Buratai da tawagar sa wucewa a Zaria.
Kungiyar kare hakkin jama’a sun yi tir da kisan, kuma sun shigar da kara a Kotun Duniya.
Ana tsare da El-Zakzaky da matar sa Zeenat, bayan an kashe ‘ya’yan sa hudu a wancan farmaki da sojoji suka kai gidan sa.
Sau da dama kotu tarayya na bayar da beli da kuma cewa a saki malamin, amma gwamnatin tarayya ta yi biris da wannan umarnin.
Ikirarin da Lai ya yi na ciyar da Sheikh El-Zakzaky abincin naira milyan 3.5 a kowane mako, ya zo ne a rana daya da aka sake gabatar da malamin a wata kotun Kaduna, kuma aka hana belin sa.
Wani bidiyo ne aka rika watsawa inda aka nuno Lai ya na wannan ikirari ga manema labarai.
PREMIUM TIMES ta tabbatar da cewa Lai ya yi maganar da bakin sa, amma ya umarci ‘yan jarida cewa kada su buga, magana ce kawai tsakanin sa da su, ba don su bayyana ba.
Ministan na Yada Labarai ya yi wannan furuci ne a lokacin da ya ke gabatar da wani taron manema labarai na hadin guiwa, shi da Ministan Harkokin Sufuri, Rotimi Amaechi, wanda har ya sa baki a cikin raha, ya ce, “to kun ga ma da a kurkuku ya ke tsare, bai fi gwamnati ta rika kashe masa naira 500,000 a wata ba, inji Amaechi.
Lai ya ce ana kashe masa wadancan makudan kudade ne, da nufin ya nuna yadda ake kulawa da shi sosai.
Sai dai kuma dimbin jama’a sun shiga shafukan su na sada zumuntar tweeter, su na caccakar ministan.
Da yawa na cewa karya ya ke kantarawa, kamar yadda suke yawan zargin sa a yawanci kalaman da ya kan furta wajen kare muradun gwamnatin tarayya.
Idan maganar Lai gaskiya, hakan na nufin a kowace rana aka ciyar da El-Zakzaky abincin naira 115,000 kenan.
Wannan ne jama’a ke ta fadin ra’ayoyin su a soshiyal midiya su na cewa ba gaskiya ba ne.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA ,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source:  Premium Times Hausa

Sunday, 28 October 2018

KARANTA KAJI: JIHOHI GUDA BIYU A KASAR NIGERIA BAZASU TAƁA ZAUNAWA LAFIYA BA

KARANTA KAJI: JIHOHI GUDA BIYU A KASAR NIGERIA BAZASU TAƁA ZAUNAWA LAFIYA BA

Wadannan jahohi bazasu taba samun zaman lafiya ba har sai sun dawo ga tirbar da aka san su da ita.


1. JAHAR BORNO

2. JAHAR ZAMFARA.

Marubuci: Mansur Musa Mancy Wanzamai

Wadannan jahohi bazasu taba samun zaman lafiya ba har sai sun dawo ga tirbar da aka san su da ita.

jahar borno, duk Africa idan akazo fannin sanin ilimin qur'ani basuda na biu. Allah ya azurtasu da masana littafin sa mai tsalki amma sai suka maida qur'anin Allah abun yin sihiri da tsibbace-tsibbace, tare da amfani da ayoyin ubangiji ta mummunar hanya.

Shin kuna ganin Allah zai barsu haka, ba tare da ya jarabce su da ukubar sa ba !!!?

Haka kuma, Zamfara, Wadda akeyiwa kirari da "Noma da shari'a sune tunkahon mu," itace jaha ta farko a duk Africa data nunawa duniya cewa tayi alkawalin tafiyar da dukkanin lamurran ta abisa tsarin shariar musulunci.

Aka kafa shari'a, ko kuma ince aka jaddadata, amma daga bisani sai muka yaudari kawunan mu, mukayi watsi da shari'ar nan, harma munayiwa Allah izgikl, muka dauki kalamar "shari'a" wata kalma ta yaudarar al'umma.

Yau jahar zamfara takai matakin da duk wani kalar zunubi da aka aikatawa a Nigeria zamfara ta lunka shi.

Shin kuna ginin Allah zai kyale jahar zamfara ba tare da ya addabe mu da musibu kala-kala ba !!!?.

Ina mai rantsuwa da Allah akan cewa, wallahi Idan da zaa kawo dukkanin Africa a jahohin zamfara da borno bazasu iya kawar da wadannnan musibu da suka addabe mu ba har sai mun farfado daga barcin da mukeyi.

Gwamnati bazata iya kawo muna zaman lafiya ba, har sai mun dawo ga Allah.

Yazama dole ga malamai suyiwa gwamnati bore domin dawo da martabar Shari'a a jahar zamfara.

Yazama dole malaman Nigeria su yaki matsibbatan da suka addabi jahar borno idan har anson zaman lafiya ya wanzu a kasar mu Nigeria.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA ,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: www.MuryarHausa24.com.ng

Thursday, 25 October 2018

Karanta Kaji: Dan Nijeriya Ya Lashe Gasar Cin  Dandakakken Nama Mai Mugun Yaji A Kasar Sin (China) - Karanta Yadda Abin Yafaru

Karanta Kaji: Dan Nijeriya Ya Lashe Gasar Cin Dandakakken Nama Mai Mugun Yaji A Kasar Sin (China) - Karanta Yadda Abin Yafaru

An karrama ɗan Nijeriyar da ya ci gasar da lambar yabo abin ya ƙayatar da mutane sosai gwanin ban sha'awa.


Wannan gasa mutane daga ƙasashe biyar ne suka shiga domin gwada sa’arsu ta cinye wani dandaƙakƙen nama mai dankaren yajin barkono.

An karrama ɗan Nijeriyar da ya ci gasar da lambar yabo.

Kamar yadda Majiyar mu Rariya ta ƙara da Cewa"Sai dai kuma dukkan waɗanda suka shiga gasar sun gaza cinye abincin yayin da shi ɗan Nijeriya ya cinye ya kuma suɗe kwanon."

Mabiya shafin Muryar Hausa24 Idan bazaku manta ba wannan dai bashi bane karo na farko da 'yan Nijeriya suke nuna irin bajintar su a ƙasashen Duniya, wanda hakan ke ƙara bunƙasa sunan a wasu yankunan na ƙasashen ƙetare.

Duk da cewa, Nijeriya ta kasance giwar kasashen da akewa laƙabi da sunan Afrika (Africa) , waɗanda mafiya mutanen da suke cikin ƙasashen akasarin su baƙaƙen fatane, wanda wasu suke ganin sunan afrika tamkar yana nuni da ƙasashen baƙaƙen fatane kawai anasu ganin.

Koma dai me ne ne,  Muryar Hausa24 muna yiwa kasashen mu fatan nasara Allah kuma ya ci gaba da tsare mana ƙasashen Mu daga sharrin masu Sharri Amin.

Karanta Kaji: Wani Bawan Allah ya yiwa wanda ya kirkiri Tuwo da Miyan kuka Allah ya isa

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA ,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode