Showing posts with label LABARAN HAUSA. Show all posts
Showing posts with label LABARAN HAUSA. Show all posts

Thursday, 7 March 2019

MAHAIFIYAR SHEIHK DAURAWA TA RASU

MAHAIFIYAR SHEIHK DAURAWA TA RASU

Inna lillah Wa Inna ilaihi Rajiun Allah Ya Yiwa Mahaifar Sheikh Aminu Daurawa Rasuwa Za'ayi Janaiza A gidansaa Na Unguwar 'Yar Akwa Kusa Da Darussunnah Ko Makarantar Zam - Zam Da Misalin Karfe Sha Daya Na Safe Insha Allahu.
KAR KU YADDA A RUDE KU DA BATUN BIDIYON GANDUJE

KAR KU YADDA A RUDE KU DA BATUN BIDIYON GANDUJE

Don Allah kowa ya daure ya karanta wannan rubutun har karshe, kafin a bayyana ra'ayi ko fahimta, banda zagi da cin mutuncin juna.
Bayan na gama tattara dalilai na 'yan adawa da suke sukar Maigirma Gwamnan jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da shi, gaba daya abin da suke sukarshi a kai bai wuce batun wani faifan bidiyon zargi wanda 'dan jaridarsu ya fitar ba.
Wannan ne dalilin da yasa na yanke shawarar shiga rigar 'yan sanda masu binciken manyan laifuka domin na warware mana tsakanin zare da abawa akan bidiyo na zargi irin wannan da 'dan jarida ya fitar akan Gwamna Ganduje, zanyi cikakken bayani a bisa mizanin ka'idoji na bincike.
Idan aka dauki bidiyon 'dan jaridar 'yan adawan Gwamna sai aka aza akan ka'idar "Forensic analysis" to a gaskiya babu alaka tsakanin wannan bidiyo na zargi da shi Maigirma Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, ko da kuwa bidiyon na gaskiya ne ba a na'ura mai kwakwalwa aka tsarashi ba, kamar yadda 'yan ta'adda suke zama a cikin daki su tsara bidiyon farfaganda.
Dalilin da yasa nace babu alaka tsakanin wannan bidiyon zargi da shi Maigirma Gwamna Abdullahi Umar Ganduje shine idan akaje yanke hukunci a gaban alkali akwai wasu abubuwa na gaskiya (fact ingredients) da suke kan doron doka da dole sai sun shiga cikin bidiyon kafin a yarda da alakarsa da Maigirma Gwamna Ganduje.
Idan akace "wanda ake zargi da aikata laifi" (crime suspect) to sai an hada abubuwa da dama kafin a yarda a amince da cewa an aikata laifi, misali:-
Waye ya aikata laifin (suspect)?
A ina aka aikata laifin (scene of crime)?
Wanda aka aikatawa laifin (victim)
Shaida sahihiya (factual evidence)
Dole sai wadannan abubuwa sun hadu kafin a tabbatar da an aikata laifi jama'a a dokar Nigeria kuma kusan haka yake a dokar musulunci.
Musamman ita shaida sahihiya itace alkali ke dogaro da ita ya tabbatar da an aikata laifi, misali:-
-Ina shaidar Gwamna Ganduje ya karbi kudin cin hanci? amsa shine ga bidiyo da 'dan jarida ya fitar amma watakila ba kudin cin hanci bane yake karba sakone ko kuma tallafi ne aka bashi
-Shin bidiyon sahihi ne? amsa babu tabbacin haka domin har an saka wakar sharewa a cikin bidiyon
-Waye ya mika kudin da ake zargi na cin hanci ne? amsa babu, kuma ba'a sanshi ba, ba'a nuna fuskarsa ba
Wadannan abubuwa ne da dole sai an tabbatar da gaskiyarsu a matsayin shaida kafin ace Gwamna ya aikata laifin karban cin hanci, wannan ka'ida na karban shaida sahihiya shine abinda alkalan musulunci suke cewa "Qarina mu'allaqah" a turance "circumstantial evidence"
A ka'idar tattara shaida sahihiya, akwai abinda ake kira da gurbacewa ko gurbatacciyar shaida (contamination of evidence), ita wannan gurbacewar shaida tana faruwa ne duk lokacin da akace ga sahihiyar shaida, sai akace an kara wani abu akan shaidar, ko kuma an rage wani abu akan shaidar, musamman shaida da ake nema na abinda ya shafi alaka da na'ura mai kwakwalwa ko laifukan yanar gizo (Cyber crimes), da zaran an samu kari ko ragi to shaida ta lalace jama'a.
Saboda haka ku lura a farkon bidiyon da 'dan jaridar 'yan adawa ya fitar na zargin Maigirma Gwamna na karban cin hanci sai akaji wata karar sharewa na tashi a cikin bidiyon, wannan ya nuna cewa anyi editing bidiyon aka kara wani abu, don haka shaidar gaskiyan bidiyon ko da sahihi ne to ya lalace a ka'idah.
Ya ku jama'ar Kano kar ku yarda a rudeku da wannan bidiyo wanda 'dan jaridar 'yan adawa ya fitar don cimma burin su na siyasa, a rubutun da nayi a baya na fada muku cewa 'yan adawa da suka tashi fitar da bidiyon (wanda ni dai ban yarda da sahihancinsa ba) sai sukayi amfani da 'dan jaridarsu saboda su samu kariya na dokokin aikin jarida ko da ya tabba karyane da sharri da batanci to ba zai fuskanci hukunci mai tsanani a gaban alkali ba, iyakaci yayi rubutun bayar da hakuri yace an samu kuskuren aikin jarida, shikenan magana ya kare.
Kanawa kar ku yarda a raba tsakaninku da gwamna Abdullahi Umar mai kokarin kwatanta gaskiya da adalci, mai halin dattako wanda ya dauko hanyar gina sabuwar jihar Kano, kar ku yarda a rabaku dashi, idan Allah Ya kaimh ranar asabar ku fito ku bashi kuri'ah don ya zarce.

Wednesday, 6 March 2019

Ko An Samo Maganin Cutar HIV AIDS Kuwa,?

Ko An Samo Maganin Cutar HIV AIDS Kuwa,?

An kasa gano cutar AIDS daga jikin wani mutum mai dauke da cutar bayan da aka yi masa dashen sabbin kwayoyin halitta, kuma wannan ne karo na biyu da likitoci suka yi irin wannan gwajin.
A yanzu dai, marar lafiyan da ke zaune a birnin Landan ya daina nuna alamun cutar tsawon wata 18 kuma ya daina shan magungunan cutar.
Sai dai masu bincike na ganin cewa akwai sauran lokaci kafin a ce marar lafiyan ya warke gaba daya.
Masana dai na ganin wannan wani mataki ne mai muhimmanci a gano maganin cutar AIDS.
Wasu masana ne daga Jami'o'in Landan da Imperial da Cambridge da kuma Oxford suka hada kai wajen yin wannan aikin.
Wannan ne karo na biyu da wani mai dauke da cutar ya warke ta wannan hanyar.
Shekaru goma da suka wuce, aka yi wa wani mai dauke da cutar dashen bargo daga wani wanda ba ya dauke da cutar.
Sinadarin CCR5 shi ne ke bai wa kwayar cutar HIV damar shiga cikin kwayoyin halittar dan Adam.
Sai dai akwai 'yan tsirarun mutane a duniya da ba sa iya kamuwa da cutar AIDS saboda ba a halicce su da sinadarin CCR5 din ba.
Ana yi wa mai dauke da cutar HIV dashen kwayoyin halitta daga mutumin da ba ya dauke da sinadarin CCR5.
An yi wa marar lafiyan na Landan dashen kwayoyin halitta daga jikin daya daga cikin irin mutanen da ba su da CCR5 kuma daga nan sai jikinsa ya gaza daukar kwayar cutar HIV din.
Sai dai ana iya samun kwayoyin cutar HIV din kadan a jikin sai dai ba za su yi wani tasiri ba.
Farfesa Graham Cooke na Makarantar Nazarin Lafiya ta Birtaniya kuma mai nazari kan cututtukan da ake iya dauka a Kwalejin Imperialde ke Landan ya ce sakamakon wannan dashe ya kara masu kwarin gwiwa.

Tuesday, 5 March 2019

Kotu Ta Soke Duk Wasu Tuhume-Tuhumen Da Take Wa Marigayi Alex Badeh

Kotu Ta Soke Duk Wasu Tuhume-Tuhumen Da Take Wa Marigayi Alex Badeh

Babbar Kotun Tarayya Reshen Abuja, ta soke dukkan tuhume-tuhumen badakalar wawurar kudade da EFCC ke yi wa tsohon Ministan Tsaro, marigayi Alex Badeh.
Wasu ‘yan bindiga ne suka bindige Badeh a cikin shekarar da ta gabata, a kan hanyar sa bayan ya dawo daga gonar sa a jihar Nassarawa.
Babban Mai Shari’a Okon Abang ya soke karar da tuhume-tuhumen a cikin hukuncin da ya bayar, wanda aka samu kamfanin Badeh mai suna Iyalikam Nigeria Limited da shi Badeh din kan sa da aikata laifukan da aka caje shi.
Ana tuhumar sa ne da laifuka 10 da suka jibinci wawurar kudaden makamai a lokacin gwamnatin Goodluck Jonathan.
Kotu ta umarci cewa dukkangidajen da aka samu a hannun Badeh, a mallaka su ga gwamnatin tarayya ta hannun EFCC.
Mai Shari’a ya kuma ci gaba da cewa a shaida wa Hukumar Rajistar Masana’antu da Kamfanoni ta Kasa wannan hukunci da kotun ta yanke.
“Tunda ya amsa laifin sa, kuma ya amayar da abin da aka amince zai amayar din, to na yanke hukuncin cewa an kama shi da laifi.
“Tunda kuma wanda ake tuhumar ya rigaya ya musu bayan ya amsa laifin sa, kuma ya amince zai maido kadarorin, to daya yau an soke kuma na kashe dukkantuhume-tuhumen da kotu ke yi masa.
Obi Thanks Nigerians For Their Votes, Explains Reason For PDP Going To Court

Obi Thanks Nigerians For Their Votes, Explains Reason For PDP Going To Court

The running mate to the PDP Presidential candidate, Alhaji Atiku Abubakar, in the just concluded presidential elections, has thanked Nigerians for their support for the PDP during the election.
Speaking to the press in his Onitsha home yesterday, Mr. Peter Obi said he was touched by the eagerness with which Nigerians came out to fulfill their civic duties of voting. He thanked especially the youth and women, some of whomexercised their voting rights for the first time in the over 119,000 polling booths scattered all overNigeria.
Obi also condoled the families of those that lost their lives and those that sustained various degrees of injuries during the election. He appealed to them not to allow their spirit become dampened towards the performance of their civic duties in future.
Speaking on the general conduct of the election, Obi said it was anything but a transparent, free and fair election, which certainly fell far below the standard established by the 2015 Presidential Election saying that it was characterize by deliberate voters’ suppression and intimidation throughout the South-East and South-South, actions he described as the highest form of corruption.
Obi lamented that the two zones under reference witnessed different sets of rule. According to him, "While some zones voted strictly using the card readers, other zones, as part of the manipulation orchestrated by the ruling party, APC were allowed to vote without card readers contrary to the guidelines INEC issued before the election."
On the way forward, Obi said he aligned fully with PDP as a party, the Presidential candidate, Alhaji Atiku Abubakar and well-meaning Nigerians in condemning the exercise.
Obi added that as law abiding citizens, that the PDP as a party, its Presidential candidate and himself, had decided to go to court because of their belief in the rule of law. “Though elections give citizens a means to hold their leaders accountable by voting incumbents out of office or promising to hold to account those leaders successfully elected, the process is more important than the outcome as the rule of law must always prevail. Thus, the consequences of Nigeria without rule of law will be unimaginable chaos and tyranny.”
Expressing his confidence in the judiciary, Obi said he appreciated the intervention of well-meaning Nigerians on the issue.
However,concerning those that advised against going to court, Obi said that the dilemma of Nigeria was allowing impunity to go unchallenged.
" Besides putting a stop to impunity", Obi said, " such a challenge will also go a long way in strengthening the electoral processes and in guarding against repetition of such dastardly acts in future.
Obi who recalled how he had been on the route before, called on Nigerians to have faith in the judiciary as the last hope of a common man.
The PDP Vice Presidential Candidate cautioned against witch-hunting of opposition leaders and more especially voters in some parts of the country who voted according to their conscience. He said “To the young people, millions of whom I came across on our campaigns across the length and breadth of this country, and who showed great enthusiasm and promise for a greater Nigeria, I urge you to troop out on Saturday, March 9 to restate your message of a desire for a better Nigeria. Though a few as shown by ballot snatching, and violence are still held down by tribalism and ethnic bigotry, I urge the majority to continue in the march of the New world order, where all are equal, and Nigeria is United, secure and Prosperous.
An Gano Manya Manyan Dalilan Da Suka Sa Atiku Ya Fadi Zabe

An Gano Manya Manyan Dalilan Da Suka Sa Atiku Ya Fadi Zabe

A halin yanzu dai za a iya cewa karshen tika-tika-tik, domin tuni jama'ar Najeriya suka fara mantawa da zaben shugaban kasa da aka gudanar wanda shugaban kasar Muhammadu Buhari ya yi zarra.
Fafatawar da aka yi a zaben ta kunshi 'yan takara 73 amma jam'iyyu biyu ne suka fi shahara watau jam'iyyar APC mai mulki da babbar jam'iyyar adawa ta kasar watau PDP.
Masana kan harkokin siyasa sun dade suna fashin baki a kan yadda zaben zai kaya ganin cewa dukkanin 'yan takarar biyu da suka fi shahara watau Muhammadu Buhari da kuma Atiku Abubakar suna da magoya baya a sassa daban daban na kasar.
Amma a karshe Atiku Abubakar ya sha kaye sakamakon wasu dalilai da ke da alaka da dan takarar.
Wadannan dalilai kuwa sun hada da:
1. Ikirarin sayar da NNPC
Da dama daga cikin al'ummar Najeriya na mamaki kan yadda Atiku Abubakar ya furta kalaman cewa ko da za a kashe shi sai ya sayar da babban kamfanin mai na Najeriya watau NNPC.
Ana ganin kamar subutar baki ce Atiku ya yi da fadin wadannan kalamai amma dan takarar yana sane ya fadi hakan.
Matsalar ita ce bai fito fili ya yi wa 'yan kasar bayanin me yasa zai sayar da kamfanin ba.
Haka ma bai gamsar da mutane da za su fito su bayyana kwararan hujjoji musamman a gidajen rediyo da talabijin domin wayar da kan jama'ar kasar ba, kuma hakan ya jawo aka yi wa wannan kudurin nasa mummunar fahimta.
Wadannan kalaman da ya yi 'yan jam'iyyar APC sun yi amfani da su domin kushe Atiku Abubakar wajen yakin neman zabe kuma 'yan kasar sun amince da hakan.
Abin da dan Najeriya yake kallo shi ne idan an sayar da kamfanin mai na kasar kudin mai zai karu kuma a ganinsa ita kadai ce kadarar da ta rage da yake amfana da ita.
Tun kafin wannan zaben 'yan kasar na zargin Atiku Abubakar wajen cefanar da manyan kadarorin kasar kamar su kamfanin wutar lantarki na NEPA da kuma kamfanin sadarwa na NITEL.
2. Guguwar Buhari
Guguwar Buhari kalma ce da ta samo asali tun 2003 a Najeriya a lokacin da shugaban ya fara takara a jam'iyyar CPC.
A Najeriya an yi itifakin cewa babu wani dan takara a tarihin kasar da yake tara jama'a da kuma yake da goyon bayan jama'a kamar Shugaba Buhari.
A 2011 duk da cewa Shugaba Buhari bai samu mulki ba, jam'iyyarsa ta CPC ta ciwo kujeru da dama a fadin kasar, sai kuma a 2015 guguwar ta shugaban kasar ta lashe kujeru kamar wutar daji.
'Yan kasar na ganin kwatanta Buhari da wani dan takara a wannan lokaci abu ne mai wahala sakamakon irin farin jinin da Allah ya bashi.
Wuraren da ake ganin guguwar Buhari ta kayar da Atiku a jihohi uku ne, da suka hada da jihar Katsina inda Buhari ya samu kuri'u 1,232,133 sai kuma Atiku ya samu 308,056 kusan tazarar kuri'u 924,077 kenan.
Sai a jihar Kano Buhari ya samu kuri'u 1,464,768 sai kuma Atiku ya samu kuri'u 391,593 kusan tazarar kuri'u 1,073,175 kenan aka samu.
Sai kuma a jihar Borno Buhari ya samu kuri'u 836,496 sai kuma Atiku ya samu kuri'u 71,788 kusan bambancin kuri'u 764,708 kenan.
Wannan alama ce da har yanzu akwai sauran guguwar Buhari a Najeriya kuma bisa dukkan alamu ta rutsa da dan takarar PDP Atiku Abubakar.
3. Zargin cin hanci da rashawa
Duk da cewa har yanzu a Najeriya babu wata kotu da ta taba gurfanar da dan takarar ta DP Atiku Abubakar gaban kotu, 'yan kasar da dama suna yi masa zargin cin hanci da rashawa.
Atiku Abubakar dai ya taba zama mataimakin shugaban Najeriya na shekaru 8 karkashin mulkin PDP inda ake zargin a wannan lokacin ne ya azurta kansa.
'Yan kasar da dama suna zargin cewa ya mallaki kamfanoni da masana'antu da gidaje a fadin Najeriya da kuma kasashen ketare a lokacin da yake da mukamin mataimakin shugaban kasa.
Wannan ne yasa aka samu rashin yarda tsakaninsa da wasu daga cikin 'yan kasar inda suke ganin cewa ko da ya lashe zaben, zai azurta kansa ne kawai.
Tsohon Shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo, ya fito karara a baya inda ya zargi Atiku Abubakar da cin hanci da rashawa, inda yake cewa ba zai iya zuwa Amurka ba domin ya tafka laifi a kasar dake da alaka da karbar rashawa.
Wannan kalamai na Obasanjo duk da cewa ya yi su ne shekaru da dama amma a lokacin wannan zabe sun yi tasiri kwarai dagaske domin kuwa jam'iyyar APC ta yi amfani da wannan domin kara kushe Atiku da kuma bayyanawa Najeriya cewa akwai kashi a gindinsa ta batun cin hanci da rashawa.
Duk da cewa daga baya Atiku ya samu shiga Amurka tare da Shugaban Majalisar Dattawa Bukola Saraki, 'yan kasar da 'ya'yan jam'iyyar ta APC sun ce Atiku ya shiga Amurkar ne a matsayin mai taimakawa shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki shi yasa kasar basu kama shi ba.
4. Ikirarin azurta abokansa da 'yan uwansa
Wani abu da Atiku ya dauka kamar da wasa ya zama babbar matsala a gare shi shi ne batun da ya yi na cewa zai azurta abokansa da 'yan uwansa.
Domin ya ce idan ya ci zabe zai azurta su, kuma kalaman sun zamo abin da aka yi amfani da su domin kayar da shi a lokacin zabe.
Akasarin 'yan kasar sun tsorata da wadannan kalamai na Atiku domin suna ganin cewa kamar Allah ne ya matse bakinsa ya fadi abin da zai yi idan ya samu nasarar lashe zabe.
'Yan Najeriya na zargin masu mulki da dama a kasar ba ma Atiku kadai ba inda suke danganta su da 'ramin kura,' daga ita sai 'ya'yanta.
Wadamnan kalamai na batun azurta abokansa da 'yan uwansa sun jawo muhawarara kwarai da gaske musamman a kafafen sada zumunta.

Sunday, 3 March 2019

El-CLASSICO: Dan Madrid Ya Kashe Dan Barcelona a Birnin Kano

El-CLASSICO: Dan Madrid Ya Kashe Dan Barcelona a Birnin Kano

Wani matashi a birnin Kano ya burma wa abokin sa wuka, jim kadan bayan tashi daga wasan da Real Madrid ta sha kashi da ci daya mai ban-haushi a hannun abokiyar adawarta, Barcelona.
Kisan ya faru ne ranar Asabar a lokacin da suka rukume gardama bayan tashi daga wasan, wanda suka kalla a cikin unguwar Yakasai, cikin birnin Kano.
An yi wasan ne ranar Asabar da dare, inda gardama ta rukume tsakanin Abdullahi Haruna da abokin sa Mujitapha Musa a kan wasan da suka rigaya suka kalla.
Ba a dai san takamaimen kalmomin da suka furta wa juna ba har Abdullahi ya burma wa abokin na sa Mujitafa wuka ba.
Baya ga kashe Mujitafa da ya yi, sai da Abdullahi ya ji wa wani mai suna Murtala Musa ciwo da wukar a guiwar sa.
Kakakin yada labaran ‘yan sanda na jihar Kano, ya shaida wa ‘yan jarida cewa an garzaya da Mujitafa da Murtala asibitin Murtala Mohammed da ke Kano, inda likita ya shaida musu cewa Mujitafa ya mutu.
Ya kara da cewa shi kuma Murtala ya na samun sauki a asibitin.
Kakakin ya ce tuni jami’an su sun cafke Abdullahi, kuma za a gurfanar da shi a gaban kotu.
Sambo Dasuki Na Nan A Raye Bai Mutu Ba, Cewar Hukumar DSS

Sambo Dasuki Na Nan A Raye Bai Mutu Ba, Cewar Hukumar DSS

Hukumar tsaro ta farin kaya, DSS ta karyata labarin da ake ta yadawa cewa tsohon mai bai shugaban kasa shawara kan sha'anin tsaro Kanal Sambo Dasuki ya rasu.
Kakakin hukumar Peter Afunanya ya shaida wa kafar talabijin ta kasa NTA cewa labarin karya ne ake yada wa, yana mai cewa "ba wai yana raye ba ne kawai, yana kuma cikin koshin lafiya."
Ya kuma yi Allah wadai da labarin wanda ake ta yadawa a intanet, tare da yin kira ga jama'a su yi watsi da shi.
Sambo Dasuki ya shafe fiye da shekaru uku a tsare. Tun watan Disamban 2015 hukumar DSS ke tsare da shi kan zargin wawushe kudin da aka ware domin sayo makaman yaki da Boko Haram.
Ana ci gaba da tsare Dasuki ne duk da kotun Tarayya ta sha ba da shi beli, har da kotun ECOWAS.
Gwamnatin Buhari dai ta dade tana cewa tana ci gaba da rike shi ne saboda ta daukaka kara.
'Yan jaridar da suka ziyarci inda ake tsare da shi sun ce sun yi tozali da shi, inda suka jima suna hira har ya amince aka dauki hotonsa domin karyata labarin ya mutu.
Buhari Tamkar Uba Yake A Gare Ni, Ni Ba Makiyinsa Ba Ne, Cewar Sanata Dino Melaye

Buhari Tamkar Uba Yake A Gare Ni, Ni Ba Makiyinsa Ba Ne, Cewar Sanata Dino Melaye

Duk wanda ya sake kallona a matsayin makiyin Buhari na bar shi da Allah, cewarsa
"Ni ba makiyin Buhari bane, da' nake a gare shi. Kowa yana sane da irin gwagwarmayar da na yi a shekarar 2015. Tare muka zagaye jihohin kasar nan baki daya, kuma ni ne kakakinsa a yayin yakin neman zabe. Na kuma jagoranci zanga-zanga zuwa ofishin INEC a madadinsa.
"Don haka a yanzu duk wanda ya kira ni a matsayin makiyin Buhari na bar shi da Allah.
Baya ga haka tunda mahaifina ne kuma shugabanmu, ba Annabi ba ne mutum ne kamar kowa, idan ya yi kuskure dole a yi masa gyara", cewar Sanata Dino Melaye.

Sunday, 24 February 2019

Buhari Ya Yi Nasara A Mazabar Lamidon Adamawa : 2019

Buhari Ya Yi Nasara A Mazabar Lamidon Adamawa : 2019

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya yiwa Wazirin Adamawa kuma dan takarar kujerar shugaban kasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar, mugunyar kayi a rumfar zabe ta mazabar fadar Lamidon Adamawa da ke karamar hukumar Yola ta Kudu.
Alkalin zaben, Idris Yunusa, yayin bayyana wannan sanarwa ya zayyana yadda shugaba Buhari dan takara na jam'iyyar APC ya lashe kuri'u 228 yayin da Atiku na jam'iyyar PDP ya samu kuri'u 138 a rumfar zabe ta 10 dake unguwar Mbamoi.
Kamar yadda kamfanin dillancin labarai na kasa ya ruwaito, baya ga samun nasara a mazabar sa ta Sarkin Yara da ke garin Daura a jihar Katsina, shugaban kasa Buhari ya kuma lallasa Atiku a mazabar sa ta unguwar Ajiya da ke birnin Yola.
A jiya mun kawo muku cewar Atiku ya gaza kawo akwatin sa yayin da shugaba Buhari ya lallasa shi da kuri'u 186, inda shi kuma ya tashi da kuri'u 167.
Sule Lamido Ya Fita Kunyar PDP Da Atiku a Mazabar Sa A Zaben 2019

Sule Lamido Ya Fita Kunyar PDP Da Atiku a Mazabar Sa A Zaben 2019

A jiya, Asabar, 23 ga watan Fabarairu ne aka gudanar da zaben shugaban kasa da 'yan majlisar tayya ('yan majalisar wakilai da dattijai) a fadin kasar nan.
Tun a jiyan sakamako su ka fara fitowa daga mazabu daban-daban da ke fadin kasar nan. Sai dai har yanzu hukumar zabe ta kasa (INEC) ba ta fara fitar da sakamako a hukumance ba.
Zaben dai ya fi jan hankali ne a matakin kujerar shugaban kasa tsakanin manyn ‘yan takara; shugaba Buhari a jam’iyyar APC da babban abokin hamayyar sa, Atiku Abubakar, dan takarar jam’iyyar PDP.
Manema labarai da ‘yan jarida sun fi mayar da hankali a kan sakamakon mazabun manyan ‘yan siyasa da ke goyon bayan ‘yan takarar biyu.
Wata majiyar mu daga jihar Jigawa ta sanar da mu cewar tsohon gwamnan jihar, Alhaji Sule Lamido, ya fita kunyar jam’iyyar PDP da dukkan ‘yan takarar ta na kujerar shugaban kasa da na majalisar tarraya.
Tsohon gwamnan ya kada kuri’ar sa a mazabar sa ta Bamaina ‘C’ da ke garin Bamaina a karamar hukumar Birnin Kudu.
A matakin kujerar shugaban kasa jam’iyyar PDP ta samu kuri’u 259 yayin da APC ta samu kuri’u 20.
Jam’iyyar PDP ta samu kuri’u 278 a zaben kujerr dan takara Sanata yayin da APC ta samu 6. A matakin kujerar majalisar wakilai PDP ta samu kuri’u 267 yayin da APC ta samu 17.

Friday, 22 February 2019

INEC Ta Bi Umurnin Kotu Ta Anshi Yan Takarar Jam'iyyar APC Na Jihar Zamfara

INEC Ta Bi Umurnin Kotu Ta Anshi Yan Takarar Jam'iyyar APC Na Jihar Zamfara

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bayyana cewa za ta yi aiki da umurnin kotun daukaka kara dake zamanta a birnin tarayya Abuja da ta soke hukuncin babbar kotun tarayya da ta hana a saka yan takarar jam'iyyar APC a jihar Zamfara bisa gaza aiwatar da zaben fitar da gwani da hukumar zabe INEC ta bayar da adadin kwanakin kaidar da ya kamata a kammala shi.
A sanarwar da INEC din ya yi a shafinta na Twitter ta ce a yanzun yan takarar jam'iyyar APC tun daga matakin Gwamna da yan majalissar tarayya da kuma na jihohi za a kara da su a cikin zaben da za a fara gudanarwa daga gobe Asabar 23 ga watan February 2019
Sai dai hukumar zaben ba ta bayyana bangaren ko wadanne yan takarar ne za ta saka a cikin zaben ba, kasantuwar yadda yan bangaren Gwamnan jihar mai barin gado Abdulaziz Yari, da bangaren Sanata Kabiru Marafa kowa ke bayyana cewa yan takararsa ne ke kan kaida.
'Yan sanda ke tsaron rumfar zabe ba sojoji ba - INEC

'Yan sanda ke tsaron rumfar zabe ba sojoji ba - INEC

Hukumar zaben Najeriya INEC ta ce 'yan sanda ne ke da hakkin kula da rumfunan zabe ba sojoji ba.
Shugaban hukumar INEC ne Farfesa Mahmood Yakubu ya bayyana haka a lokacin yake bayani kan shirin zabe da kuma amsa tambayoyi a ranar Alhamis.
An tambayi shugaban INEC ne kan irin rawar da sojoji za su taka a ranar zabe, sai ya amsa da cewa tsarin da aka sani shi ne, ba hakkin sojoji ba ne kula da tsaro a rumfunan zabe, amma ya danganta da gayyatar da suka samu daga 'yan sanda.
Ya ce hukumar INEC na aiki ne da hukumar 'yan sanda amma idan suna fuskantar wata barazana suna iya gayyato sauran jami'an tsaro da suka hada da sojoji domin su taimaka.
"Sojoji na iya yin aikin da ya rataya a wuyan 'yan sanda a wurin zabe idan har 'yan sandan sun gayyace su."
"Ya danganta da barazanar da ta taso amma aikin tabbatar da tsaro a rumfunan zabe aikin 'yan sanda ne," in ji shugaban hukumar INEC.
Wannan na zuwa ne bayan babban hafsan sojin kasa na Najeriya Janar Tukur Buratai, a ranar Laraba ya bayyana rawar da sojoji za su taka a ranar zabe.
Yayin da yake gana wa da manyan jami'ai da kwamandojin sojin kasar, Janar Burutai ya yi umurni ga kwamandojinsa su dauki mataki na ba sani ba sabo kan duk wanda ya nemi dagula sha'anin zabe a kasar.
Ya ce rundunar sojin kasar ta dauki mataki kan satar akwati da kayayyakin zabe da aka saba yi a zabukan baya.
Tun da farko shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi gargadi ga barayin akwatin zabe inda ya umurci jami'an tsaron kasar daukar matakin ba sani ba sabo na rashin tausayi ga duk barawon akwatin zaben da suka kama.

Thursday, 21 February 2019

Babu Wanda Zai Mani Kawanya Idan Na Hau Kujerar Shugaban Kasa - Atiku

Babu Wanda Zai Mani Kawanya Idan Na Hau Kujerar Shugaban Kasa - Atiku

Dan takarar kujerar Shugaban kasa a karkashin jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya bayyana cewa ba zai bari wasu mutane da ake kira da ‘cabal’ su mulki gwamnatinsa ba idan har ya lashe zaben ran Asabar, 23 ga watan Fabrairu.
Atiku, wanda ya bayyana hakan yayinda yake zantawa da masu ruwa da tsaki daga kananan hukumomi 23 na jihar Kaduba, yace gaba daya juya gwamnatin Shugaban kasa Muhammadu Buhari wasu ke yi, inda yayi zargin cewa hakan ne ya sanya kasar cikin kangin wahala da wuya da take ciki a yanzu.
Atiku yace ko kadan PDP ba za ta yarda da sace akwatunan zabe ba kuma ba za ta dauki kowani mataki da ya saba doka ba, inda yace bayar da umurnin kashe duk wanda ya sace akwatin zabe ba damokradiyya bane.
Tsohon mataimakin Shugaban kasar yace idan har aka zabe shi a ranar Asabar mai zuwa toh zai siyar da NNPC domin samar da Karin ci gaba, inda yace a yanzu mutane kalilan ne ke amfana daga ayyukan kadarorin kasar maimakon yan Najeriya baki daya.

Tuesday, 19 February 2019

JAMB 2019 Exam Slip Reprinting Begins 2nd March

JAMB 2019 Exam Slip Reprinting Begins 2nd March

JAMB has disclosed that the printing of 2019 JAMB Exam Slip would commence March 2nd, 2019; that is two weeks before the examination. The reprinted slips will bear candidates schedule for the examination: date, time and centre as well as other necessary information about the examination.
According to the board, from March 2nd, candidates will have their slips placed on their profiles. However candidates who are unable to access their slips through their portal can visit the board’s service portal,onhttp://www.jamb.org.ng/to print the slip.

Friday, 15 February 2019

United State (US) Secretary of State, Calls Atiku, Congratulates Him Ahead of the Polls

United State (US) Secretary of State, Calls Atiku, Congratulates Him Ahead of the Polls

The United State (U.S) Secretary of State, Secretary Mike Pompeo just got off a call with the PDP presidential candidate; Alhaji Atiku Abubakar, where he congratulated him and reaffirmed the International Community’s commitment to free and fair election in Nigeria. Recall that Mr. Pompeo is the most senior officer in the Trump administration and while it is based on speculation, Atiku Abubakar allegedly met with Donald Trump on his visit to the Trump Towers in Washington D.C.
Pundits have pointed out the tacit support the US has given the right-lining Atiku Abubakar who promises to create jobs by reducing taxes and encouraging inflow of FDI into Nigeria. The Chief of Staff to the APC candidate; Abba Kyari, had published a letter accusing the International Community of supporting the emergence of Atiku Abubakar in the forthcoming election. Atiku had already signed a Peace Accord alongside Muhammadu Buhacri, with the both agreeing to concede defeat if they lose in a credible poll.

Monday, 11 February 2019

Kungiyar Tijjaniyya Movement Ta Yi Kira A Zabi Buhari

Kungiyar Tijjaniyya Movement Ta Yi Kira A Zabi Buhari

Kungiyar Tijjaniyya SUFI Movement ta yi kira ga mabiyanta a duk fadin Nijeriya cewa a sake zabar Buhari karo na biyu, domin an gwada shi an ga kuma nagartarsa.
A jawabin da kungiyar ta fitar ga manema labarai, shugaban kungiyar na kasa , Timasaniyu Ahmed-Rufai, ya ce sake zabar Buhari a Nijeriya alheri ne bisa ayyukan alkairan da ya shinfidawa kasar nan.
Kungiyar ta kuma lissafo dalilanta na tsayar da Buhari a matsayin dan takarar da za su zaba saboda ayyukan hanya da na ci gaban al'umma da aka yi karkashin gwamnatin shugaban kasa Muhammad Buhari.
An Kama Mutum 50 Kan Rikicin Siyasar Jihar Kano

An Kama Mutum 50 Kan Rikicin Siyasar Jihar Kano

Rundunar 'yan sanda ta jihar Kano a Najeriya ta ce ta yi nasarar kama mutane 50 da take zargi da bangar siyasa da kwace a yayin taron siyasa da aka gudanar na PDP a jihar ranar Lahadi.
"Babu wanda ya fi karfin doka kuma duk mukaminsa sai mun hukunta shi, don doka gaba take da kowa", in ji kwamishinan 'yan sanda na jihar Wakili Mohammed.
"Babu yadda za a yi a ce wasu tsuraru su ji sun fi karfin doka.
"Don haka mun hana yawo da kowane irin makami, kuma mun hana fita da 'yan banga yawon yakin neman zabe." inji Wakili.
Har wa yau, ya kuma ce rundunar 'yan sandan jihar za ta sanya kafar wando daya da masu sayar da kwaya da kayan maye a jihar. Wakili Mohammed ya ja hankalin iyaye da su ja kunnen 'ya'yansu kan shiga bangar siyasa don guje wa fushin hukuma.
Yanayin siyasa a jihar Kano na kara munana duk da yarjejeniyar da yan takara suka sanya wa hannu kan yakin neman zabe da gudanar da zaben cikin lumana a jihar.
A ranar Lahadi ne 'yan daba suka rika far wa mutane tare da yi masu kwace jim kadan bayan ziyarar da dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar ya kai jihar Kano domin yakin neman zabe.
Lamarin da ya jawo asarar rayuka da tare da ji wa mutane munanan raunuka.

Thursday, 7 February 2019

MALAMAN ALKUR'ANI SUN YI JAN KUNNE GA TASHAR AREWA24 Cikin Shirin (DADIN KOWA)

MALAMAN ALKUR'ANI SUN YI JAN KUNNE GA TASHAR AREWA24 Cikin Shirin (DADIN KOWA)

Muna kallon shirin dadin kowa Muna kallon yadda kuka shirin Yaki da Malaman AL-QURANI domin tozarta ALMAJIRCI Ta hanyar dora malam NA TA'ALA (MATO YAKUBU) da bashi damar tozarta AL QUR'ANI kai tsaye domin wata manufa ta yahudu akan Almajirci da nunawa wadanda ba musulmai ba su fahimci dukkan malamin AL QUR'ANI a matsayin mutum me son zuciya da son kai wadda bai isa akan komai ba.
JAN KUNNE
A matsayin mu makusanta makaranta AL- QUR'ANI muna kira da babbar murya cewa ya zama dole a gyara ko kuma muma mu daura dammarar yaki daku a makarantun mu na zaure da tsangayu da islamiyyu ta hanyar aika muku da ADDUO'I na musamman har sai ALLAH YAYI MANA MAGANINKU.
JAN KUNNE GARE KA WATO YAKUBU (NA TA'ALA) (Allah Ya Shirya).
Ya zama dole ka gyara irin siffofin da kake siffanta makaranta AL QUR'ANI domin cimma manufarka ta tozarta malaman AL QUR'ANI da wulakantasu ka sani cewa ka shirya fito na fito ne da LITTAFIN ALLAH dukkan wadda ya shirya haka babu shakka ya durfafi hanyar fito na fito ne da MAHALICCIN WANNAN LITTAFI ALLAH (SWT).
KIRA GA MUTANE MUSAMMAN MA MAKARANTA AL- QUR'ANI Mutaimaka Wajen Yada Wannan Saqo Har Ya Isa Ga Masu Shirya Wannan Shiri Wato Hukumar Gidan Area24.
Muhammad Ahidan Bako Arifullah
Allah Ya Kwauta.
ASUU Ta Janye Dogon Yajin Aikin Da Ta Shiga Tsawon Wata Uku

ASUU Ta Janye Dogon Yajin Aikin Da Ta Shiga Tsawon Wata Uku

Kungiyar Malaman Jami'o'i Nijeriya ASUU ta janye dogon yajin aikin da ta shiga tun kusan watanni ukun da suka gabata.
Yajin aikin na zuwa ne bayan dogon zaman da suka yi na kulla yarjejeniya tsakanin su da jami'an gwamnatin tarayya, karkashin jagorancin ministan kwadago Cris Ngige.
Sannnan kungiyar ta ASUU ta umurci malamanta da su koma bakin aiki daga gobe Jumu'a 8 February 2019.