Showing posts with label Labarai. Show all posts
Showing posts with label Labarai. Show all posts

Tuesday, 4 June 2019

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Sa'ad Muhammad Yayi Sanarwa.

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Sa'ad Muhammad Yayi Sanarwa.

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Sa'ad Muhammad Yayi Sanarwa.

Labarin da muke kawo muku kai tsaye daga fadar mai alfarma sarkin Musulmi, Sultan Abubaakar Sa'ad na nuna cewa an ga sabuwar jaririyar watar Shawwal, a yau Litinin 29 ga watan Ramadan wanda yayi daidai da 3 ga watan Yuni, 2019.
Sarkin Musulmi ya sanar da cewa gobe, ranar Talata ce 1 ga watan Shawwal kuma Sallar Idi
Yace: Bisa ga shari'ar Musulmi, muna masu sanar muku da cewa a yau Litinin 3 ga watan Yuni 2019 wanda yayi daidai da 29 ga watan Ramadan 1440, ne karshen watan Ramadana na shekarar 1440AH."
"Mun samu rahotannin tabbacin ganin wata daga shugabannin adinin Musulunci daga gari daban-daban.. Mai martaba Shehun Borno, Sarkin Gwandu, Sarkin Jema'a, Sarkin Damaturu, da wasu sa sassan jihar sokoto
Bisa da haka, gobe Talata 4 ga watan Yuni, 2019 ta zama 1 ga watan Shawwal 1440AH kuma ranar Sallah. Muna rokon Allah ya karba ibadun da mukayi a cikin watar Ramadan."
Source: Legit
Rikici ya barke tsakanin Fati Muhammed da Teema Makamashi akan soyayyar Sanata Dino Melaye.

Rikici ya barke tsakanin Fati Muhammed da Teema Makamashi akan soyayyar Sanata Dino Melaye.

Rikici ya barke tsakanin Fati Muhammed da Teema Makamashi akan soyayyar Sanata Dino Melaye.

An dai ga Teema Makamashi tana habaici a shafinta na Instagram inda
Duka 'yan matan sun yiwa Sanatan waka da fasta ta siyasa sun kai masa, inda ya dauki hoto da kowaccen su
Wani rikici da ya barke tsakanin matan Kannywood guda biyu Teema Makamashi da Fati Mohammed, inda suke rikici akan Sanatan jihar Kogi ta Yamma Sanata Dino Melaye.
Rikicin ya samo asali ne lokacin da Teema Makamashi take gargadin Fati Mohammed akan kwaikwayenta da tayi wurin yiwa Sanatan waka.
Ga abinda Teema Makamashi ta rubuta a shafinta na Instagram:
"Keda samun soyayyarsa sai dai ki gani daga nesa"
Tauraruwar Teema Makamashi wacce ita ce ta fara yiwa Sanata Dino Melaye waka, tayi wannan habaicin ne ga Fati Mohammed wacce ta kwafeta.
Teema tayi rubutun ne a shafinta na Instagram inda ta cigaba da cewa, "Ga wani sabon salon shima idan zaki yi, banda waka, tunda kome nayi sai kinyi, kina tare da bakar wahala indai ni zaki dinga kwaikwaya.

Friday, 17 May 2019

Gwamnatin Jihar Kano Zata Yiwa Sarkin Kano Muhammadu Sanusi <> Canji Masarauta A Gobe Asabar.

Gwamnatin Jihar Kano Zata Yiwa Sarkin Kano Muhammadu Sanusi <> Canji Masarauta A Gobe Asabar.

Gwamnatin Jihar Kano Zata Yiwa Sarkin Kano Muhammadu Sanusi <> Canji Masarauta A Gobe Asabar.


Rahotonnin da suke shigo mana na nuni da cewar, a gobe Asabar ne gwamnan Kano Ganduje zai yiwa Mai Martaba Sankin Kano Muhammadu Sanusi II canjin masarauta.
Majiyar mu, wadda wani makusancin gwamnatin da ya nemi a sakaye sunansa, ya shaidawa wakilin mu cewar, gwamnatin ta gama shirinta tsaf gobe Asabar domin mayar da Sarki Sanusi II Bichi tare da maye gurbin masarautar ta Kano da sabon Sarkin Bichi Aminu Ado Bayero.
Majiyarmu hausaloaded ta ruwaito wannan labari daga madubi h Saidai da muke jin ra'ayin jama'a, mafiya yawa sun bayyana rashin goyan bayansu akan wannan abinda yake faruwa tsakanin masarautar Kano da gwamnatin jihar Kano.

Saturday, 11 May 2019

Yar gidan Sarkin Kano ta mayarwa da Ganduje raddi.

Yar gidan Sarkin Kano ta mayarwa da Ganduje raddi.

Yar gidan Sarkin Kano ta mayarwa da Ganduje raddi.

Tayin da gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya kammala kacaccala jihar zuwa masarautu biyar, sai gashi diyar Sarkin Kano, Fulani Siddika ta yiwa gwamnan raddi akan abinda ya yiwa mahaifinta
Bayan kaddamar da karin masarautun yanka guda hudu a Kano da gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya yi, 'yar gidan Sarkin Kano Muhammad Sanusi II ta yi wani raddi a shafinta na Instagram.
A bayanin da ta yi, duk da yake an goge, amma 'yar uwarta Fulani Siddika, ta sake sanyawa, inda ta bayyana gwamnan Kano Ganduje a matsayin "Bala'i da Allah ya kawowa mutanen Kano".
'Yar gidan Sarkin Kano ta mayarwa da Ganduje raddi
Ga abinda ta ce a shafin nata:
"Idan kuna so ku ga me rashin asali ke jawo wa ku duba ku ga abinda Ganduje yake yi a Kano. Mutumin da bashi da wata daraja, amma yana kokarin ya ja da mutanen da suke da daraja. Ina addu'ar Allah yasa kada mahaifiyata ta ce na goge wannan bayanin a shafina. Ganduje shi ne bala'in da yafi komai a jihar Kano. Abinda yake yi a gwamnatinsa, son rai ne kawai a ciki. Bamu kamaci gwamnati irin wannan ba. Allah ya raba mu da masifar Ganduje dan kuwa mutanen da basu da asali sune suke bata masu asali.
Bugu da kari, Shahida ta kara rubuta cewa, Da zarar Sarki ya tsorata da rasa kujerar sa, abinda yake yi shine ya sauke kansa,
Babu shakka a cikin bayanin da ta yi a shafin nata Fulani Siddika, ta rubuta cewa
Ba ni da wani abu da zan cegaskiya!" 'Yar'uwata ce ta fada duka.

Sources:hausaloaded

Thursday, 9 May 2019

Rabi,u sheriff usman baba Allah yayi masa rasuwa a yau hudu ga watan ramadan.

Rabi,u sheriff usman baba Allah yayi masa rasuwa a yau hudu ga watan ramadan.

Rabi,u sheriff usman baba Allah yayi masa rasuwa a yau hudu ga watan ramadan.

Da sanyin safiyar yau Alhamis hudu 4 ga watan Ramadan, wanda yayi daidai da tara 9 ga watan Mayu na wannan shekarar, Allah yayiwa fitaccen Sha'irin nan wato Sheriff Rabi'u Usman Baba rasuwa.
Majiyar mu ta ruwaito cewa za'a gudanar da jana'izar fittacen Sha'irin kamar yada addinin Muslunci yatanadar a gidansa dake kofa ta biyu (second gate) dake unguwar Janbulo a cikin birnin Kano.
Rabi'u Usman Baba ya shahara wajen rera wakokin yabo ga fiyayyen Halitta Annabi Muhammad (S.a.w) da iyalansa inda har yaciri tutar zama shugaban kungiyar Shu'ara'ul Islam ta Najeriya baki daya kafin rayuwarsa.
Daruruwan jama'a na cigaba da bayyana alhininsu game da mutuwar fitaccen Sha'irin tare da jimamin rashin sa, duba yadda wakokin sa sukayi tasiri a tsakanin mabiya darikar Tijjaniyya da kuma Kadiriyya.

Fatan Allah yagafarta masa

Sunday, 5 May 2019

Anga Watan Ramadan a Makka.

Anga Watan Ramadan a Makka.

Anga Watan Ramadan a Makka.

Labari yazo ta bangare da yawa cewa anga wata a makka haka anganshi a sokoto da jigawa.

Thursday, 25 April 2019

Wednesday, 24 April 2019

Kalli hotunan ÆŠalibin  mafi kyawun rubutun hannu a duniya

Kalli hotunan ÆŠalibin mafi kyawun rubutun hannu a duniya

Kalli hotunan ÆŠalibin  mafi kyawun rubutun hannu a duniya


A cikin wani sakon da kwanan nan ya sake yi a kan kafofin watsa labarun, masu amfani da kafofin watsa labarun sun yi bikin Prakriti Malla, bayan bayanan da hannunta ya ba shi damar shiga yanar gizo.

Wani mai amfani da Twitter wanda aka gano kamar yadda Ahmed ya raba wani tweet wanda ya bayyana cewa Malla, wanda yake dan aji 8 wanda ya fito daga Nepal, an ba shi damar karbar takarda mafi kyau a duniya.

Friday, 19 April 2019

JAMB: 2019 UTME ƙare, 'yan takara ku shirya don fara duba sakamakon.

JAMB: 2019 UTME ƙare, 'yan takara ku shirya don fara duba sakamakon.

JAMB: 2019 UTME ƙare, 'yan takara ku shirya don fara duba sakamakon.

An kammala jarrabawar Matriculation Matter na shekara ta 2019 (UTME) a ​​yau, Laraba, Afrilu 17.
Fabian Benjamin, shugaban jarida da yada labaran kungiyar hadin gwiwar hadin gwiwa (JAMB), a ranar Talata ya bayyana cewa tun daga ranar 13 ga Afrilu, fiye da miliyan 1.2 sun samu nasarar rubuta takardun.
Fiye da 'yan takarar miliyan 1.8 ana sa ran su zauna don UTME na hukumar da ta fara a kasar a ranar 11 ga Afrilu.
Biliyaminu ya ci gaba da cewa babu wani sakamako da aka samu.
Ya bayyana cewa, hukumar tana ci gaba da nuna sakamakon sakamakon binciken da aka yi, kuma saboda an gano wasu ayyukan yaudara.
"Dole ne mu ci gaba da yin nazarin wadannan sakamakon saboda akwai wasu batutuwa da muka gano kamar labaran rikodin, wanda ba shi da alaƙa da kuma abubuwan da suke so, don haka muna har yanzu suna kama su.
"An kama wasu kuma wadanda ba a kama su ba, muna da rubuce-rubucensu, za mu yi kifi a waje. Duk da haka, 'yan takara suyi tsammanin sakamakon su ba da da ewa ba, "inji shi.

Monday, 15 April 2019

Hotunan da aka fara da biki na 'yan yaro  mai shekaru 17 da ya auri yarinyar mai shekaru 15 da haihuwa

Hotunan da aka fara da biki na 'yan yaro mai shekaru 17 da ya auri yarinyar mai shekaru 15 da haihuwa

Hotunan da aka fara da biki na 'yan yaro  mai shekaru 17 da ya auri yarinyar mai shekaru 15 da haihuwa

Hotuna na farko na Aliyu da matarsa, Aisha

Yaron mai shekaru 17 da ake kira Aliyu da yar uwarsa ko matarsa mai shekaru 15, Aisha, sun fito da hotuna kafin su yi aure, mako mai zuwa, a Sokoto.

An sake cewa Aliyu yana bin al'adun gidansu na auren da wuri. Yayan maza na iyalinsa sun auri lokacin da suke da shekaru 17, yayin da mata suna aure a 15.

Duk da haka, a cikin matsanancin hali, sun yi aure lokacin da suke da shekaru 19. An ce ana bin al'adun don hana su yin fasikanci da kuma ba su damar ganin jikoki.

Wednesday, 6 March 2019

Ko An Samo Maganin Cutar HIV AIDS Kuwa,?

Ko An Samo Maganin Cutar HIV AIDS Kuwa,?

An kasa gano cutar AIDS daga jikin wani mutum mai dauke da cutar bayan da aka yi masa dashen sabbin kwayoyin halitta, kuma wannan ne karo na biyu da likitoci suka yi irin wannan gwajin.
A yanzu dai, marar lafiyan da ke zaune a birnin Landan ya daina nuna alamun cutar tsawon wata 18 kuma ya daina shan magungunan cutar.
Sai dai masu bincike na ganin cewa akwai sauran lokaci kafin a ce marar lafiyan ya warke gaba daya.
Masana dai na ganin wannan wani mataki ne mai muhimmanci a gano maganin cutar AIDS.
Wasu masana ne daga Jami'o'in Landan da Imperial da Cambridge da kuma Oxford suka hada kai wajen yin wannan aikin.
Wannan ne karo na biyu da wani mai dauke da cutar ya warke ta wannan hanyar.
Shekaru goma da suka wuce, aka yi wa wani mai dauke da cutar dashen bargo daga wani wanda ba ya dauke da cutar.
Sinadarin CCR5 shi ne ke bai wa kwayar cutar HIV damar shiga cikin kwayoyin halittar dan Adam.
Sai dai akwai 'yan tsirarun mutane a duniya da ba sa iya kamuwa da cutar AIDS saboda ba a halicce su da sinadarin CCR5 din ba.
Ana yi wa mai dauke da cutar HIV dashen kwayoyin halitta daga mutumin da ba ya dauke da sinadarin CCR5.
An yi wa marar lafiyan na Landan dashen kwayoyin halitta daga jikin daya daga cikin irin mutanen da ba su da CCR5 kuma daga nan sai jikinsa ya gaza daukar kwayar cutar HIV din.
Sai dai ana iya samun kwayoyin cutar HIV din kadan a jikin sai dai ba za su yi wani tasiri ba.
Farfesa Graham Cooke na Makarantar Nazarin Lafiya ta Birtaniya kuma mai nazari kan cututtukan da ake iya dauka a Kwalejin Imperialde ke Landan ya ce sakamakon wannan dashe ya kara masu kwarin gwiwa.

Tuesday, 5 March 2019

Kotu Ta Soke Duk Wasu Tuhume-Tuhumen Da Take Wa Marigayi Alex Badeh

Kotu Ta Soke Duk Wasu Tuhume-Tuhumen Da Take Wa Marigayi Alex Badeh

Babbar Kotun Tarayya Reshen Abuja, ta soke dukkan tuhume-tuhumen badakalar wawurar kudade da EFCC ke yi wa tsohon Ministan Tsaro, marigayi Alex Badeh.
Wasu ‘yan bindiga ne suka bindige Badeh a cikin shekarar da ta gabata, a kan hanyar sa bayan ya dawo daga gonar sa a jihar Nassarawa.
Babban Mai Shari’a Okon Abang ya soke karar da tuhume-tuhumen a cikin hukuncin da ya bayar, wanda aka samu kamfanin Badeh mai suna Iyalikam Nigeria Limited da shi Badeh din kan sa da aikata laifukan da aka caje shi.
Ana tuhumar sa ne da laifuka 10 da suka jibinci wawurar kudaden makamai a lokacin gwamnatin Goodluck Jonathan.
Kotu ta umarci cewa dukkangidajen da aka samu a hannun Badeh, a mallaka su ga gwamnatin tarayya ta hannun EFCC.
Mai Shari’a ya kuma ci gaba da cewa a shaida wa Hukumar Rajistar Masana’antu da Kamfanoni ta Kasa wannan hukunci da kotun ta yanke.
“Tunda ya amsa laifin sa, kuma ya amayar da abin da aka amince zai amayar din, to na yanke hukuncin cewa an kama shi da laifi.
“Tunda kuma wanda ake tuhumar ya rigaya ya musu bayan ya amsa laifin sa, kuma ya amince zai maido kadarorin, to daya yau an soke kuma na kashe dukkantuhume-tuhumen da kotu ke yi masa.
Obi Thanks Nigerians For Their Votes, Explains Reason For PDP Going To Court

Obi Thanks Nigerians For Their Votes, Explains Reason For PDP Going To Court

The running mate to the PDP Presidential candidate, Alhaji Atiku Abubakar, in the just concluded presidential elections, has thanked Nigerians for their support for the PDP during the election.
Speaking to the press in his Onitsha home yesterday, Mr. Peter Obi said he was touched by the eagerness with which Nigerians came out to fulfill their civic duties of voting. He thanked especially the youth and women, some of whomexercised their voting rights for the first time in the over 119,000 polling booths scattered all overNigeria.
Obi also condoled the families of those that lost their lives and those that sustained various degrees of injuries during the election. He appealed to them not to allow their spirit become dampened towards the performance of their civic duties in future.
Speaking on the general conduct of the election, Obi said it was anything but a transparent, free and fair election, which certainly fell far below the standard established by the 2015 Presidential Election saying that it was characterize by deliberate voters’ suppression and intimidation throughout the South-East and South-South, actions he described as the highest form of corruption.
Obi lamented that the two zones under reference witnessed different sets of rule. According to him, "While some zones voted strictly using the card readers, other zones, as part of the manipulation orchestrated by the ruling party, APC were allowed to vote without card readers contrary to the guidelines INEC issued before the election."
On the way forward, Obi said he aligned fully with PDP as a party, the Presidential candidate, Alhaji Atiku Abubakar and well-meaning Nigerians in condemning the exercise.
Obi added that as law abiding citizens, that the PDP as a party, its Presidential candidate and himself, had decided to go to court because of their belief in the rule of law. “Though elections give citizens a means to hold their leaders accountable by voting incumbents out of office or promising to hold to account those leaders successfully elected, the process is more important than the outcome as the rule of law must always prevail. Thus, the consequences of Nigeria without rule of law will be unimaginable chaos and tyranny.”
Expressing his confidence in the judiciary, Obi said he appreciated the intervention of well-meaning Nigerians on the issue.
However,concerning those that advised against going to court, Obi said that the dilemma of Nigeria was allowing impunity to go unchallenged.
" Besides putting a stop to impunity", Obi said, " such a challenge will also go a long way in strengthening the electoral processes and in guarding against repetition of such dastardly acts in future.
Obi who recalled how he had been on the route before, called on Nigerians to have faith in the judiciary as the last hope of a common man.
The PDP Vice Presidential Candidate cautioned against witch-hunting of opposition leaders and more especially voters in some parts of the country who voted according to their conscience. He said “To the young people, millions of whom I came across on our campaigns across the length and breadth of this country, and who showed great enthusiasm and promise for a greater Nigeria, I urge you to troop out on Saturday, March 9 to restate your message of a desire for a better Nigeria. Though a few as shown by ballot snatching, and violence are still held down by tribalism and ethnic bigotry, I urge the majority to continue in the march of the New world order, where all are equal, and Nigeria is United, secure and Prosperous.
An Gano Manya Manyan Dalilan Da Suka Sa Atiku Ya Fadi Zabe

An Gano Manya Manyan Dalilan Da Suka Sa Atiku Ya Fadi Zabe

A halin yanzu dai za a iya cewa karshen tika-tika-tik, domin tuni jama'ar Najeriya suka fara mantawa da zaben shugaban kasa da aka gudanar wanda shugaban kasar Muhammadu Buhari ya yi zarra.
Fafatawar da aka yi a zaben ta kunshi 'yan takara 73 amma jam'iyyu biyu ne suka fi shahara watau jam'iyyar APC mai mulki da babbar jam'iyyar adawa ta kasar watau PDP.
Masana kan harkokin siyasa sun dade suna fashin baki a kan yadda zaben zai kaya ganin cewa dukkanin 'yan takarar biyu da suka fi shahara watau Muhammadu Buhari da kuma Atiku Abubakar suna da magoya baya a sassa daban daban na kasar.
Amma a karshe Atiku Abubakar ya sha kaye sakamakon wasu dalilai da ke da alaka da dan takarar.
Wadannan dalilai kuwa sun hada da:
1. Ikirarin sayar da NNPC
Da dama daga cikin al'ummar Najeriya na mamaki kan yadda Atiku Abubakar ya furta kalaman cewa ko da za a kashe shi sai ya sayar da babban kamfanin mai na Najeriya watau NNPC.
Ana ganin kamar subutar baki ce Atiku ya yi da fadin wadannan kalamai amma dan takarar yana sane ya fadi hakan.
Matsalar ita ce bai fito fili ya yi wa 'yan kasar bayanin me yasa zai sayar da kamfanin ba.
Haka ma bai gamsar da mutane da za su fito su bayyana kwararan hujjoji musamman a gidajen rediyo da talabijin domin wayar da kan jama'ar kasar ba, kuma hakan ya jawo aka yi wa wannan kudurin nasa mummunar fahimta.
Wadannan kalaman da ya yi 'yan jam'iyyar APC sun yi amfani da su domin kushe Atiku Abubakar wajen yakin neman zabe kuma 'yan kasar sun amince da hakan.
Abin da dan Najeriya yake kallo shi ne idan an sayar da kamfanin mai na kasar kudin mai zai karu kuma a ganinsa ita kadai ce kadarar da ta rage da yake amfana da ita.
Tun kafin wannan zaben 'yan kasar na zargin Atiku Abubakar wajen cefanar da manyan kadarorin kasar kamar su kamfanin wutar lantarki na NEPA da kuma kamfanin sadarwa na NITEL.
2. Guguwar Buhari
Guguwar Buhari kalma ce da ta samo asali tun 2003 a Najeriya a lokacin da shugaban ya fara takara a jam'iyyar CPC.
A Najeriya an yi itifakin cewa babu wani dan takara a tarihin kasar da yake tara jama'a da kuma yake da goyon bayan jama'a kamar Shugaba Buhari.
A 2011 duk da cewa Shugaba Buhari bai samu mulki ba, jam'iyyarsa ta CPC ta ciwo kujeru da dama a fadin kasar, sai kuma a 2015 guguwar ta shugaban kasar ta lashe kujeru kamar wutar daji.
'Yan kasar na ganin kwatanta Buhari da wani dan takara a wannan lokaci abu ne mai wahala sakamakon irin farin jinin da Allah ya bashi.
Wuraren da ake ganin guguwar Buhari ta kayar da Atiku a jihohi uku ne, da suka hada da jihar Katsina inda Buhari ya samu kuri'u 1,232,133 sai kuma Atiku ya samu 308,056 kusan tazarar kuri'u 924,077 kenan.
Sai a jihar Kano Buhari ya samu kuri'u 1,464,768 sai kuma Atiku ya samu kuri'u 391,593 kusan tazarar kuri'u 1,073,175 kenan aka samu.
Sai kuma a jihar Borno Buhari ya samu kuri'u 836,496 sai kuma Atiku ya samu kuri'u 71,788 kusan bambancin kuri'u 764,708 kenan.
Wannan alama ce da har yanzu akwai sauran guguwar Buhari a Najeriya kuma bisa dukkan alamu ta rutsa da dan takarar PDP Atiku Abubakar.
3. Zargin cin hanci da rashawa
Duk da cewa har yanzu a Najeriya babu wata kotu da ta taba gurfanar da dan takarar ta DP Atiku Abubakar gaban kotu, 'yan kasar da dama suna yi masa zargin cin hanci da rashawa.
Atiku Abubakar dai ya taba zama mataimakin shugaban Najeriya na shekaru 8 karkashin mulkin PDP inda ake zargin a wannan lokacin ne ya azurta kansa.
'Yan kasar da dama suna zargin cewa ya mallaki kamfanoni da masana'antu da gidaje a fadin Najeriya da kuma kasashen ketare a lokacin da yake da mukamin mataimakin shugaban kasa.
Wannan ne yasa aka samu rashin yarda tsakaninsa da wasu daga cikin 'yan kasar inda suke ganin cewa ko da ya lashe zaben, zai azurta kansa ne kawai.
Tsohon Shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo, ya fito karara a baya inda ya zargi Atiku Abubakar da cin hanci da rashawa, inda yake cewa ba zai iya zuwa Amurka ba domin ya tafka laifi a kasar dake da alaka da karbar rashawa.
Wannan kalamai na Obasanjo duk da cewa ya yi su ne shekaru da dama amma a lokacin wannan zabe sun yi tasiri kwarai dagaske domin kuwa jam'iyyar APC ta yi amfani da wannan domin kara kushe Atiku da kuma bayyanawa Najeriya cewa akwai kashi a gindinsa ta batun cin hanci da rashawa.
Duk da cewa daga baya Atiku ya samu shiga Amurka tare da Shugaban Majalisar Dattawa Bukola Saraki, 'yan kasar da 'ya'yan jam'iyyar ta APC sun ce Atiku ya shiga Amurkar ne a matsayin mai taimakawa shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki shi yasa kasar basu kama shi ba.
4. Ikirarin azurta abokansa da 'yan uwansa
Wani abu da Atiku ya dauka kamar da wasa ya zama babbar matsala a gare shi shi ne batun da ya yi na cewa zai azurta abokansa da 'yan uwansa.
Domin ya ce idan ya ci zabe zai azurta su, kuma kalaman sun zamo abin da aka yi amfani da su domin kayar da shi a lokacin zabe.
Akasarin 'yan kasar sun tsorata da wadannan kalamai na Atiku domin suna ganin cewa kamar Allah ne ya matse bakinsa ya fadi abin da zai yi idan ya samu nasarar lashe zabe.
'Yan Najeriya na zargin masu mulki da dama a kasar ba ma Atiku kadai ba inda suke danganta su da 'ramin kura,' daga ita sai 'ya'yanta.
Wadamnan kalamai na batun azurta abokansa da 'yan uwansa sun jawo muhawarara kwarai da gaske musamman a kafafen sada zumunta.

Monday, 4 March 2019

An kashe dan  Barcelona a Kano bayan a gama wasan El Clásico.

An kashe dan Barcelona a Kano bayan a gama wasan El Clásico.

An kashe dan  Barcelona a Kano bayan a gama wasan El Clásico.

Tsohon kalubale tsakanin manyan manyan kungiyoyin kwallon kafar Catalan guda biyu, Real Madrid da FC Barcelona, ​​sun yi ikirarin rayuwar wani dan wasan Barcelona a Kano bayan karshen mako.
Wani mummunan bala'in ya faru yayin da wani mai shekaru 17 mai suna Madrid, mai suna Salisu Muhammad na Yakasai a Kano, ya ce ya kori Mujittafa Musa sau uku a kirjinsa ba da daÉ—ewa ba bayan da ya kara da FC Barcelona.
Ma'aikatan iyali sun shaida wa manema labaru cewa, mai kisan gillar ya fara kwance ga wanda aka azabtar da shi bayan wasan, kuma marigayin wanda ba a kula da shi ya shiga cikin mutuwarsa ba.
Wani mai shaida da aka gano a matsayin Suleiman bai kare shi ba daga 'yar wasan kwallon kafa mai cin gashin kansa wanda ya kori shi sau biyu a gwiwoyinsa.
Rahoton asusun na iyali ya tabbatar da cewa "masu wucewa a cikin unguwa sun kama wanda ake tuhuma suka mika shi ga 'yan sanda."
Maganar iyali ta bayyana cewa "muna fatan cewa ran da ya ragu zai sami adalci".
Da yake tabbatar da wannan mummunar lamari, Jami'in Harkokin Jakadancin Jihar, DSP Abdullahi Haruna, ya shaidawa manema labaru a cikin makon jiya cewa, jihar CID ta fara binciken kan batun.
A cewarsa, "Salisu Muhammad, mai shekaru 17, ya kori Mujittafa Musa sau uku a kirjinsa a kan wata hujja akan wasan kwallon kafa ranar Asabar da yamma."
Ya ce mutumin da ake tuhuma yana kwantar da ƙafafunsa a hedkwatar 'yan sanda na Bompai kamar haka ya sa Sulaiman ya kulla gwiwoyi.
Haruna ya bayyana cewa 'yan sanda sun gano abin da ake zargi da wanda ake zargi da shi, inda ya kara da cewa wanda ake tuhuma za a gurfanar da shi gaban kotu a lokacin da aka kammala bincike.

Sunday, 3 March 2019

El-CLASSICO: Dan Madrid Ya Kashe Dan Barcelona a Birnin Kano

El-CLASSICO: Dan Madrid Ya Kashe Dan Barcelona a Birnin Kano

Wani matashi a birnin Kano ya burma wa abokin sa wuka, jim kadan bayan tashi daga wasan da Real Madrid ta sha kashi da ci daya mai ban-haushi a hannun abokiyar adawarta, Barcelona.
Kisan ya faru ne ranar Asabar a lokacin da suka rukume gardama bayan tashi daga wasan, wanda suka kalla a cikin unguwar Yakasai, cikin birnin Kano.
An yi wasan ne ranar Asabar da dare, inda gardama ta rukume tsakanin Abdullahi Haruna da abokin sa Mujitapha Musa a kan wasan da suka rigaya suka kalla.
Ba a dai san takamaimen kalmomin da suka furta wa juna ba har Abdullahi ya burma wa abokin na sa Mujitafa wuka ba.
Baya ga kashe Mujitafa da ya yi, sai da Abdullahi ya ji wa wani mai suna Murtala Musa ciwo da wukar a guiwar sa.
Kakakin yada labaran ‘yan sanda na jihar Kano, ya shaida wa ‘yan jarida cewa an garzaya da Mujitafa da Murtala asibitin Murtala Mohammed da ke Kano, inda likita ya shaida musu cewa Mujitafa ya mutu.
Ya kara da cewa shi kuma Murtala ya na samun sauki a asibitin.
Kakakin ya ce tuni jami’an su sun cafke Abdullahi, kuma za a gurfanar da shi a gaban kotu.
Sambo Dasuki Na Nan A Raye Bai Mutu Ba, Cewar Hukumar DSS

Sambo Dasuki Na Nan A Raye Bai Mutu Ba, Cewar Hukumar DSS

Hukumar tsaro ta farin kaya, DSS ta karyata labarin da ake ta yadawa cewa tsohon mai bai shugaban kasa shawara kan sha'anin tsaro Kanal Sambo Dasuki ya rasu.
Kakakin hukumar Peter Afunanya ya shaida wa kafar talabijin ta kasa NTA cewa labarin karya ne ake yada wa, yana mai cewa "ba wai yana raye ba ne kawai, yana kuma cikin koshin lafiya."
Ya kuma yi Allah wadai da labarin wanda ake ta yadawa a intanet, tare da yin kira ga jama'a su yi watsi da shi.
Sambo Dasuki ya shafe fiye da shekaru uku a tsare. Tun watan Disamban 2015 hukumar DSS ke tsare da shi kan zargin wawushe kudin da aka ware domin sayo makaman yaki da Boko Haram.
Ana ci gaba da tsare Dasuki ne duk da kotun Tarayya ta sha ba da shi beli, har da kotun ECOWAS.
Gwamnatin Buhari dai ta dade tana cewa tana ci gaba da rike shi ne saboda ta daukaka kara.
'Yan jaridar da suka ziyarci inda ake tsare da shi sun ce sun yi tozali da shi, inda suka jima suna hira har ya amince aka dauki hotonsa domin karyata labarin ya mutu.
Buhari Tamkar Uba Yake A Gare Ni, Ni Ba Makiyinsa Ba Ne, Cewar Sanata Dino Melaye

Buhari Tamkar Uba Yake A Gare Ni, Ni Ba Makiyinsa Ba Ne, Cewar Sanata Dino Melaye

Duk wanda ya sake kallona a matsayin makiyin Buhari na bar shi da Allah, cewarsa
"Ni ba makiyin Buhari bane, da' nake a gare shi. Kowa yana sane da irin gwagwarmayar da na yi a shekarar 2015. Tare muka zagaye jihohin kasar nan baki daya, kuma ni ne kakakinsa a yayin yakin neman zabe. Na kuma jagoranci zanga-zanga zuwa ofishin INEC a madadinsa.
"Don haka a yanzu duk wanda ya kira ni a matsayin makiyin Buhari na bar shi da Allah.
Baya ga haka tunda mahaifina ne kuma shugabanmu, ba Annabi ba ne mutum ne kamar kowa, idan ya yi kuskure dole a yi masa gyara", cewar Sanata Dino Melaye.

Sunday, 24 February 2019

Buhari Ya Yi Nasara A Mazabar Lamidon Adamawa : 2019

Buhari Ya Yi Nasara A Mazabar Lamidon Adamawa : 2019

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya yiwa Wazirin Adamawa kuma dan takarar kujerar shugaban kasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar, mugunyar kayi a rumfar zabe ta mazabar fadar Lamidon Adamawa da ke karamar hukumar Yola ta Kudu.
Alkalin zaben, Idris Yunusa, yayin bayyana wannan sanarwa ya zayyana yadda shugaba Buhari dan takara na jam'iyyar APC ya lashe kuri'u 228 yayin da Atiku na jam'iyyar PDP ya samu kuri'u 138 a rumfar zabe ta 10 dake unguwar Mbamoi.
Kamar yadda kamfanin dillancin labarai na kasa ya ruwaito, baya ga samun nasara a mazabar sa ta Sarkin Yara da ke garin Daura a jihar Katsina, shugaban kasa Buhari ya kuma lallasa Atiku a mazabar sa ta unguwar Ajiya da ke birnin Yola.
A jiya mun kawo muku cewar Atiku ya gaza kawo akwatin sa yayin da shugaba Buhari ya lallasa shi da kuri'u 186, inda shi kuma ya tashi da kuri'u 167.
Sule Lamido Ya Fita Kunyar PDP Da Atiku a Mazabar Sa A Zaben 2019

Sule Lamido Ya Fita Kunyar PDP Da Atiku a Mazabar Sa A Zaben 2019

A jiya, Asabar, 23 ga watan Fabarairu ne aka gudanar da zaben shugaban kasa da 'yan majlisar tayya ('yan majalisar wakilai da dattijai) a fadin kasar nan.
Tun a jiyan sakamako su ka fara fitowa daga mazabu daban-daban da ke fadin kasar nan. Sai dai har yanzu hukumar zabe ta kasa (INEC) ba ta fara fitar da sakamako a hukumance ba.
Zaben dai ya fi jan hankali ne a matakin kujerar shugaban kasa tsakanin manyn ‘yan takara; shugaba Buhari a jam’iyyar APC da babban abokin hamayyar sa, Atiku Abubakar, dan takarar jam’iyyar PDP.
Manema labarai da ‘yan jarida sun fi mayar da hankali a kan sakamakon mazabun manyan ‘yan siyasa da ke goyon bayan ‘yan takarar biyu.
Wata majiyar mu daga jihar Jigawa ta sanar da mu cewar tsohon gwamnan jihar, Alhaji Sule Lamido, ya fita kunyar jam’iyyar PDP da dukkan ‘yan takarar ta na kujerar shugaban kasa da na majalisar tarraya.
Tsohon gwamnan ya kada kuri’ar sa a mazabar sa ta Bamaina ‘C’ da ke garin Bamaina a karamar hukumar Birnin Kudu.
A matakin kujerar shugaban kasa jam’iyyar PDP ta samu kuri’u 259 yayin da APC ta samu kuri’u 20.
Jam’iyyar PDP ta samu kuri’u 278 a zaben kujerr dan takara Sanata yayin da APC ta samu 6. A matakin kujerar majalisar wakilai PDP ta samu kuri’u 267 yayin da APC ta samu 17.