Showing posts with label SHARHIN FINA-FINAN HAUSA A YAU. Show all posts
Showing posts with label SHARHIN FINA-FINAN HAUSA A YAU. Show all posts

Thursday, 24 January 2019

Karanta Kaji: Kuskure 3 da akai a cikin Film din MATAR MIJINA tare da Sharhin Fim din

Karanta Kaji: Kuskure 3 da akai a cikin Film din MATAR MIJINA tare da Sharhin Fim din

Suna: Matar Mijina
Tsara Labari: Nazir Alkanawi
Kamfani: S.H Ea: Abdul Amart
Umarni: Sadik N. Mafia


Matar Mijina


 Jarumai: Adam A. Zango. Aisha Aliyu Tsamiya, Fati Washa, Umar Gombe, Maryam Ceeter. Da sauran su.

 A farkon fim din an nuna Mutallab (Adam A. Zango) Yana bacci a cikin daki yayin da ‘ya’yan sa Yusra da Salim suka shiga suka tashe sa don yayi Karin kumallo. Bayan Mutallab ya tashi ya kimtsa ne ya fita wajen aikin sa, a sannan ne Suwaiba (Maryam Ceeter) tazo wajen Matar sa wadda ta kasance kawa ce a wajen Suwaiba. Suwaiba ta kasance tana nuna wa Jalila (Aisha Aliyu Tsamiya) aibun auren da tayi gami da ajiye karatun tan a jami’a ta zabi aure, yayin da Jalila take nuna mata hakan ba laifi bane saboda tana jin dadin irin soyayyar da mijin ta Mutallab yake nuna mata. Suwaiba tana kokarin zuga Jalila don kada ta cigaba das akin jiki da mijin ta Mutallab saboda gudun kada ya karo mata kishiya, amma Jalila tana nuna ko da hakan ta kasance ba laifi bane zata iya zama da kowacce mace wadda mijin ta zai aura. Wata rana Mutallab ya hadu da wata budurwa Samira (Fati Washa) wadda yaji ta birge shi kuma yana son auren ta, hakan ne yasa ya fara nuna wa Samira kudurin san a son auren sa kuma cikin dan lokaci kadan Samira ta amince da bukatar sa suka fara soyayya. Mutallab ya sanar da matar sa Jalila cewar yana soyayya da Samira sai hakan bai dameta bat a nuna masa goyon bayan ta akan auren da zai kara, har ya zamana cewa Mutallab yakan hada Jalila da Samira a waya su gaisa har ma suyi hira, sannan kuma yakan dauki ‘ya’yan sa Yusra da Salim ya kais u wajen Samira su gaisa. Tun Samira tana ja baya da Jalila hart a saki jiki da ita kuma ta fahimci cewa Jalila mace ce mai son zaman lafiya wadda kuma bata damu da soyayyar da ake yi da mijin taba. Wata rana Suwaiba kawar Jalila ta fito tare da kawayen ta daga cikin makaranta sai taga Mutallab ya budewa Samira motar sa yaja sun tafi, hakan ne ya kidima tat a garzayo ta sanar da kawarta Jalila abinda idanun ta suka gani, amma sai Jalila ta nuna rashin damuwar ta akan abin duk da Suwaiba ta nuna mata cewar yarinyar da ta gani tare da Mutallab bata da nutsuwa, amma yardar da Jalila tayi da mijin ta itace tasa ta gamsu da cewar ba zai ci amanar taba. Cikin dan lokaci kadan aka bikin Mutallab da Samira ya gabato, wanda hakan yasa Jalila ta soma gayyatar jama’a da sauran dangin ta har ma ta fidda kalar ankon da za su saka ranar biki. Hakan ne yasa wasu daga cikin ‘yan uwan ta suke kokarin zuga ta don kart a amince da hakan, yayin da wasu dangin nata kuma suka yi fushi da ita suke ganin kamar bata da hankali saboda tana murna don za’a yi mata kishiya. Ana ya gobe daurin aure sai Mutallab yayiwa Jalila sallama ya koma dakin hotel tare da abokan sa don su samu sakewa saboda baya son hayaniyar jama’a ‘yan biki. Kwatsam ana tsaka da shagalin biki sai ga Suwaiba kawar Jalila ta zo ta tabbatar mata da cewar Samira amaryar da za’a kawo mata tana dauke da cutar kanjamau, saboda abokin tan a makaranta wanda ake zargin tana mu’amula dashi an gane cewar yana dauke da wannan cutar. Jin hakan ne ya tashi hankalin Jalila ta kira mijin tat a nuna kada a daura wannan auren, amma sai Mutallab yayi zaton cewa kishi take da abin sai yaki saurarar ta. Sai dai kuma tun bayan auren Samira da Mutallab sai Jalila taja jikin ta gefe ta daina mu’amula da mijin ta, sannan kuma taki amincewa akan ya kusance ta saboda tana ganain cewa shima ya kamu da wannan cuta ta kanjamau. Hakan ne yasa ko ya kwana a kan gadon ta sai ta cire shimfidar gadon ta kona saboda kyankyamin sad a take yi. Ganin abinda ke faruwa ne yasa Mutallab ya soma nadamar karin auren da yayi saboda baya son abinda ke faruwa tsakanin sad a Jalila. Hakan ne yasa ya kira iyayen Jalila don su tuhume ta akan abubuwan da take yi masa, a sannan ne Jalila ta basu labarin abinda Suwaiba kawarta ta gaya mata, jin hakan ne kuma yasa Samira ta karyata cewar tana dauke da cutar kanjamau, wannan daalilin ne kuma yasa aka je asibiti akayi gwaji wanda ya tabbatar da cewa Samira da Mutallab bas u da wannan cuta ta kanjamau. Faruwar hakan c eta sa Jalila tayi nadama kuma ta roki gafarar mijin tad a ta Samira, wanda hakan yasa lokacin da Suwaiba ta sake zuwa gidan suka hadu gaba daya sukayi mata duka don kokarin kawo karshen munafurcin ta.

 Abubuwan Birgewa:

 Labarin ya tafi kai tsaye har ya adire bai karye ba.

Sunan fim din ya dace da labarin.

 Daraktan yayi kokari wajen tafiyar da labarin ta hanyar da ta dace, haka kuma yayi kokari wajen ganin cewa jaruman sun isar da sakon da ya dace, domin sun yi kokari wajen isar da sakon da ya dace. Hoto ya fita sosai, haka ma sauti ba laifi.

   Kurakurai:

 Bayan auren Mutallab (Adam A. Zango) da amaryar sa Samira (Fati Washa) me kallo ya gan su a wani falo na daban wanda bai yi kama da gidan sa da aka fara bayyanawa a fim din ba, sannan kuma yanayin da aka nuna kamar dama a gidan suke, shin canja gida suka yi? Idan kuma gidan bangare biyu ne to ya kamata tun a farko a bayyanawa me kallo, duk da dai yanayin yadda aka bayyana tsarin gidan a baya bai yi kama da cewar bangare biyu bane.

Lokacin da Jalila (Aisha Tsamiya) ta sami labarin cewa amaryar da mijin ta zai aura tana dauke da cutar kanjamau, me kallo yaga tana guje masa domin ko zama a inda yake bat a yi, wanda bayan ya kwanta akan shimfidar ta ma sai ta kona zanin gadon duk da shima zanin gadon bata taba shi da hannu ba har sai da ta sa leda ta rufe hannuwan nata, sannan ta dauka ta kona, shin Jalila ba ta san cewa ba a daaukar cutar kanjamau ta hanyar zaman takewa da masu cutar ba? Tun da an nuna cewar tana da ilimin addini da na zamani gami da fahimta, bai dace kuma a nuna cewar ta kona shimfidar da mijin ta ya kwanta ba don gudun kamuwa da cutar da take zargin sad a ita.

Lokacin da Jalila ta fara fadawa kawarta Suwaiba labarin cewa mijin ta zai kara aure, bayan tafiyar Suwaiba me kallo yaji muryar ta a waya sa’in da ta kira Jalila tana sanar da ita cewar yarinyar da mijin ta zai aura tana saka hotunan sa Instagram, haka zata zuba idanu bazata dau mataki ba, shin ya akayi Suwaiba ta gane cewar amaryar da za’a auro tana saka hotunan Mutallab a Instagram alhalin a sannan bat a san sunan tab a kuma bata ga ma hoton tab a balantana ayi zaton ko a sannan ta san ta? Ya dace a samar da dalili kafin faruwar hakan. 

Karkarewa:

Fim din ya fadakar domin an nuna illar daukar zugar kawaye tare da kuma illa ga budurwa mai sakin jiki da maza a waje wanda hakan yakan ja mata mugun zargi.

Haka kuma an nuna darasi ga wasu matan ta hanyar nuna musu ba laifi bane don mijin su zai kara aure. Wallahu a’alamu!



Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: www.MuryarHausa24.com.ng


Tuesday, 8 January 2019

Karanta Kaji: Kuskure 3 da akai a cikin Film din RUDANI tare da Sharhin Fim din

Karanta Kaji: Kuskure 3 da akai a cikin Film din RUDANI tare da Sharhin Fim din

Suna: Rudani
Tsara Labari: Nasir S. Gwangwazo da Jamilu Ahmad Yakasai
Kamfani: Almubarak International Films Production Limited 
Shiryawa: Abubakar Bashir Mai Shadda Umarni: Ahmad A. Bifa 
Jarumai: Ali Nuhu, Jamilu Ahmad Yakasai, Ibrahim Mandawari, Aisha Aliyu Tsamiya, Rukayya Umar, Hajara Usman, Hadiza Muhammad da dai sauransu 



Sharhi: Hamza Gambo 

A farkon fim din an nuna Baba (Ibrahim Mandawari) ya shigo gidan sa iyalan sa sun tarbe shi suna yi masa murnar karin shekarar haihuwar sa. An nuna cewar yana zaune da matar sa (Hajara Usman) tare da ‘ya’yan sa Yaya Bashir (Ali Nuhu) da kanin sa Sadik (Jamilu Yakasai) wadanda suma suke tare da matayen su a cikin gidan. Duk da kasancewar shi Sadik suna samun rashin jituwa da matar sa Habiba (Aisha Aliyu Tsamiya) wadda tsananin kishin sa da take yi yasa har ta fara zargin sa akan yana bin matan banza, hakan yasa lokacin da zai tafi London taki amincewa da tafiyar sa saboda tana zargin cewa ba aiki zai tafi ba zai je ne kawai don ganawa da budurwar sa baturiya. Sun samu rashin jituwa a sanda mijin nata Sadik zai bar kasar duk da kasancewar yayi mata bayanin aikin da zai kaishi London din amma ta kasa fahimta. 

Bayan tafiyar Sadik London sai Habiba ta soma rashin lafiya, amma bayan zuwan ta asibiti sai aka tabbatar mata da cewar tana dauke da larurar cuta mai karya garkuwar jiki wato kanjamau. Jin hakan ne ya tashi hankalin Habiba ta kara tabbatar da zargin da take yiwa mijinta na cewar yana neman matan banza. Bayan ta dawo gida ta sanar da iyayen sa sai aka kira sa aka bukaci yaje asibiti acan London din don a auna jininsa don a gane ko yana dauke da cutar shima, amma sai Sadik yaki amincewa da hakan har a karshe mahaifin sa ya bukaci yabar aikin da yake ya dawo gida domin a sannan rigima ce ta afku iyayen Habiba suna neman mika maganar zuwa kotu don a bi wa ‘yar su hakkin ta. Hakan ne yasa Sadik ya dawo gida najeriya aka je wajen likita ya duba jinin sa, sai dai bisa mamaki da aka duba sai aka gane cewar babu cutar kanjamau din a jikin sa. Hakan ne ya sake haifar da hargitsi domin iyayen Habiba sun ki yarda da binciken da akayi saboda suna zargin cewa a jikin sa ne Habiba ta dauki cutar kanjamau. A karshe dai dangin Habiba suka kai Sadik asibitin da suke ganin za’a fada musu gaskiya, sai dai kuma acan din ma sakamakon iri daya ne bayanai sun tabbatar da cewar Sadik bashi da cutar kanjamau, hakan ne yasa zargin kowa ya koma kan Habiba, domin ta jima da guduwa gidan iyayen ta, acan din ne mahaifiyar ta (Hadiza Muhammad) ta rutsa ta da tambayar inda ta kwaso cutar kanjamau, sai dai kuma Habiba ta gaza bata amsa. Ana tsaka da haka ne Sadik yaje gidan su Habiba ya fada mata gaskiyar cewa baya mu’amula da matan banza kuma budurwar sa ta kasar waje sun jima da rabuwa domin saurayin ta yayi masa gargadin kada ya sake ganin su tare. Bayan Sadik ya gama bawa Habiba labari ne sai ya bukaci da tayi dai tunani don a gane inda ta samu larurar kanjamau, ya bata misalin cewar ba sai ta hanyar jima’i ake daukar cutar ba, akan iya samun ta ta hanyar yankan farce ko kitso ko wani dalili daban na haduwar jini. Jin hakan ne yasa Habiba ta bashi labarin cewa wata rana kawarta tazo gidan ta tun tana amarya ta bata shawara akan yin tsarin iyali don kada ta haihu da wuri, sai dai kuma bayan zuwan su asibitin sai likita ya tabbatar musu da cewar sirinji daya ne ya rage wanda za’a yi musu allura, sai dai ya fita ya siyo wani, amma sai duk su Habiba suka nuna sauri suke yayin da kawar ta ta bukaci cewar tunda su kawaye ne a yi musu da guda dayar kuma a fara yi mata sannan a yiwa Habiba, hakan kuwa akayi nan aka fara yi mata allurar sannan aka yiwa Habiba. Bayan Habiba ta gama ba shi labari sai Sadik yaje neman kawar Habiba a gidan ta amma sai ya samu labarin cewa ita da mijin ta sun rasu kuma ana zargin cutar kanjamau ce ta kashe su. 

Wannan dalilin ne yasa aka gane inda Habiba ta samu larurar cutar kanjamau, kuma Sadik yayi alkawarin zai kai ta London don nema mata magani kuma idan ta warke yayi alkawarin zai mayar da ita dakin sa.

 Abubuwan Birgewa

1- Labarin ya fadakar kuma ya tafi kai tsaye har ya dire bai karye ba, sannan kuma an yi kokarin saka abubuwan da suka rike mai kallo har zuwa karshen labarin. 

2- An yi kokari sosai wajen samar da muhallin da su ka dace da labarin wato (locations)

 3- Daraktan ya yi kokari sosai wajen tafiyar da labarin ta hanyar da ta dace, haka yayi kokari wajen ganin jaruman sun taka rawar da ta dace, domin jaruman sun yi kokari musamman Habiba wato Aisha Tsamiya.

 4- Sauti ya fita radau, haka ma hoton fim din ya fita radau domin an yi kokari wajen nuna salon daukar hoton fim din.

 Kurakurai

1- An nuna cewar tun Habiba ta na amarya kawarta ta raka ta wajen yin allurar tsarin iyali (wato family planning) wanda dalilin hakan ne ya sa a ka samu matsalar da Habiba ta kamu da larurar cutar kanjamau, sai dai kuma duk da a na daukar cutar ta hanyar jima’ai kuma an nuna cewar Sadik ya na tare da matar tasa har na tsahon lokaci, amma shi bai kamu da wannan larurar ba, ya dace a nuna wa mai kallo dalilin da ya sa Sadik bai kamu da cutar ta kanjamau ba.

 2- Lokacin da Sadik ya bawa Habiba labarin budurwarsa wadda su ka yi soyayya a kasar waje, me kallo ya ga Sadik ya dauki budurwar tasa a can kasar London ya kai ta gidan wata dattijuwa wadda ya kira da Mom. Shin wace ce wannan dattijuwar wadda Sadik ya kai budurwarsa gidan ta a London? Tun da an nuna mahaifiyarsa a Najeriya (wato Hajara Usman). To, ya dace a yiwa me kallo bayanin matsayin dattijuwar nan a wajen sa ko da ta hanyar nuna cewar ‘yar uwar mahaifin sa ko mahaifiyar sa ce

 3- Shin ina mahaifin Habiba? Har fim din ya kare mai kallo bai gan shi ba kuma ko a baki ba a ambace shi ba, duk da kasancewar akwai matsaloli da yawa na fannin auren Habiba da suka taso wanda ya kamata ace an ga mahaifin ta a cikin maganar, amma ba a gan shi ba sai wani Barrister da aka nuna a matsayin kawun su. Idan ma mutuwa mahaifin ta yayi to ya dace ko a baki ne a fada. 

Karkarewa:

Fim din ya fadakar kuma labarin ya tafi kai tsaye zuwa ga sakon da ake son isar wa. An nuna illar bin shawarar kawaye, sannan kuma an yi kokari wajen isar da wani muhimmin sako wanda al’umma zasu amfana da shi, domin fim din ya koyar da wani darasi wanda jama’a zasu kiyaye rayuwar su da lafiyarsu. 

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode


Source: LEADERSHIP A YAU



Friday, 4 January 2019

Karanta Kaji: Fitattun Fina-Finan Hausa Guda 10 Mafi Shahara a 2018

Karanta Kaji: Fitattun Fina-Finan Hausa Guda 10 Mafi Shahara a 2018

Allah Ya kara kawo masana'antar Kannywood zuwa karshen wannan shekara.



Ba ma wannan kadai ba, masana'antar ta samu ci gaba da har ta yi fina-finai iri-iri, wadanda yawanci na barkwanci da soyayya ne, da kuma almara, wadanda kalilan ne.
Daga ciki akwai fim din ban-dariya na Adam A. Zango, wato Dan Kuka a Birni da fim din Ali Nuhu da ya yi shi shekara 18 baya kuma ya sake yinsa yanzu, Mujadala, da dai sauransu.
Kabiru Jammaje, wanda shi ne musabbabin farfadowar sashen Ingilishi a Kannywood, ya sake daukar nauyin wani kasaitaccen fim din sarauta mai suna In Search of the King.
Da alamun fim din Nafisa Abdullahi, Yaki a Soyayya, ma za a ji dadinsa, saboda haka shekarar ta 2018 ta kayatar.
Wadannan fina-finan da aka jero a kasa su ne suka fi shahara da fice a wannan shekarar, wacce ta zo dab da babban zaben Najeriya wanda za a yi farkon shekara mai zuwa.
Ga shi siyasa ta kunno kai cikin masana'antar ta Kannywood, har ma ake ganin ta janyo rarrabuwar kawuna gami da barazanar kara raba kan mambobin masana'antar da ba a jima da sasanta su ba - kodayake, wannan ba shi ne maudu'inmu yanzu ba.
Fina-finan ba bisa daraja aka jera su ba:

1. Ruwan Dare





Ruwan DareHakkin mallakar hotoYASIN AUWAL
Image captionRuwan Dare ne ya yi fice a cikin fina-finan Kannywood na 2018

Fim din, wanda daraktansa shi ne Yaseen Auwal kuma ake ganin yana daya daga cikin fina-finan Kannywood da suka fi dacewa da yanayin da ake yanzu, yana shagube ne cikin salon tsoratarwa ga matasan da suka gama jami'a kuma suke raina duk wani aikin da ba na ofishi ba.
Aminu Sharif, wato Momoh, da Sadiq Sani Sadiq wasu mutane ne da suke son yin kudi ko ta wane hali kuma masu tsananin buri ne, wadanda sun gama digirinsu na farko a fannin Akanta da Tattalin Arziki.
Abokinsu kuwa, wanda shi ma ya gama jami'ar, Baballe Hayatu, ba irin salonsu ya dauko ba.
Saboda haka, daga karshe sai ya samu nasara.
Su kuma wadancan biyu daga karshe sun koyi darasi sannan suka yi nadama.
Fim din ya yi matukar haduwa saboda yadda jigonsa yake da alaka da wannan zamanin.
Kuma 'yan wasan, wadanda aka ambaci sunayensu a sama da ma wadanda ba a ambata ba, sun yi kokari sosai.
Za a iya kau da kai daga 'yan kura-kuran cikin fim din - irin su ambatar Yugoslavia a matsayin kasa, kura-kuran nahawun Turancin Ingilishi, da sauransu.

2. Rabi'atu





Maryam Yahaya a fim din Rabia'atuHakkin mallakar hotoGOOGLE
Image captionMaryam Yahaya a fim din Rabia'atu

Rabi'atu, wanda Aminu S. Bono ya yi darakta, an shirya shi ne kwata-kwata a gidaje guda uku; kuma yana nuna irin hadarin da 'yar aikin gida ke shiga a gidan da take aiki.
Maryam Yahaya, wacce ta fito a matsayin ita ce Rabi'atu, takan yi duk aikace-aikacen babban gidan Alhaji Rabiu Rikadawa, yayin da matarsa, Hadiza Muhammad, kuwa ke zuwa wajen aiki; 'ya'yansa hudu kuma makaranta suke zuwa.
Rabi'atu dai yarinya ce mai yarinta kuma kamammiya, wacce gidansu ba masu karfi ba ne.
Saboda haka kowa a cikin gidan da take aiki sonta yake yi, har ma manyan 'ya'yan gidan guda biyu suke takara da juna wajen samun karbuwar soyayya a wajenta.
Sai dai ba ta amince da su ba, tana mai jaddada musu cewa sun wuce ajinta.
Sai dai duk da haka ba wanda ya hakura a cikinsu.
Ana haka, kwatsam sai wata rana Alhaji ya zo gidan ya same ta ita kadai har ya yi lalata da ita.
Daga bisani, sai matar Alhaji ta gano Rabi'atu fa ta samu juna-biyu sakamakon lalata da Alhaji ya yi da ita.
Aka yi ta gumurzu dai har zuwa karshe.
Fim din bai ci kudi ba, amma ya yi matukar dacewa da yanayin da ake ciki yanzu.
Sannan, labarin ya yi kama da zahiri kuma daraktan da mataimakansa da kuma 'yan wasan, wadanda ba shahararru ba ne, sun yi aiki da basira sosai.
Babu rawa da waka a ciki.
Ba ma wannan ba, karshen fim din ya kayatar.

3. Fuska Biyu





Fim din Fuska BiyuHakkin mallakar hotoADAM ZANGO
Image captionFim din Fuska Biyu

Fuska Biyu yana nusarwa ne game da yadda wasu iyaye ke saurin aurar da 'ya'yayensu mata ba tare da bincike kan mazajen da za su aurar wa ba.
Fim din yana ba da labari ne na wani madugun masu garkuwa da mutane, Adam A. Zango, wanda da rana yake bayyana a matsayin mai sayar da kifi.
Amal, wata kamilalliyar yarinya, wacce 'yan uwanta ba masu karfi ba ne, takan sayar da abinci a gefen teburin da Zango ke ikirarin yana sayar da kifi.
A haka sai suka fara soyayya.
Irin abin duniya da yake ba ta ya sa mahaifiyarta take jin akwai lauje cikin nadi.
Amma mahaifinta kuma ya dage cewa 'yarsa fa ta samu mijin aure.
Sai kuma da lokaci ya kure sannan mahaifin ya fahimci kuskurensa.
Fim din akwai jan hankali cikinsa.
Yana da amfani sosai a kalle shi.

4.Risala





Fim din RisalaHakkin mallakar hotoABUBAKAR S SHEHU
Image captionFim din Risala

Sunan wannan fim, Risala, wata kalma ce ta Larabci, wacce ke nufin "sako".
Risala, wanda Abubakar S. Shehu ya yi darakta, siffofin zamanin baya yake da su.
Gogaggen tauraron nan, Sadiq S. Sadiq (Zakariyya), ya yi wata tafiya da nufin neman mutumin da ya yi wa ba-daidai ba don neman afuwa.
Tafiya ce mai cike da karaskiya, masifu da abubuwan al'ajabi.
Abin bai tsaya a haka ba - sai da ya sake haduwa da wata jarrabawa a wani gari da ake kira Baihan, garin da mutumin yake.
Wannan mutumin ya yarda zai masa afuwa amma sai in ya amince zai auri 'yarsa, wacce, a cewarsa, ta fi kowa muni a garin kuma musaka ce.
Sai Zakariyya ya amince amma ba cikin son ransa ba.
Ashe dai yarinyar nan ba haka take ba; hasali ma, yarinyar matukar kyau ne da ita.
Bayan 'yan kura-kurai da fim din ke da su kamar rashin takaita darussa da yake koyarwa, da kuma ci-da-karfi wajen aiwatar da wasu abubuwa, fim din ya dauko tarihin haihuwar shahararren malamin addinin Islaman nan ne, Abu Hanifa.
Kodayake yawancin fina-finan Kannywood kwaikwayo su ake yi daga wani waje.
Baya ga haka, sautin shirin ya dauku.

5. Hakki





Fim din HakkiHakkin mallakar hotoINSTAGRAM/HAMISU IYANTAMA
Image captionFim din Hakki

Kamar yadda ake fada, tsohuwar zuma da ita ake magani.
Sanannen kamfanin shirya fina-finai, Iyantama, shi ya yi fim din Hakki yayin da Hafizu Bello, kwararre a harkar, ya yi darakta.
Labari ne kan wani mai suna Jabir, wanda jajirtaccen ma'aikaci ne kuma dan gwagwarmaya a wani kamfanin fata.
Ba a san shi da karba ko ba da cin hanci ba.
Ba tare da nuna fargaba ba, yake yaki da rashin adalci da kuma rashin kyautawar da hukumar kamfanin ke yi wa ma'aikata.
A bangare guda kuma, akwai labarin wani gungun 'yan mata da suke janyo mazaje cikin wani loko domin abokansu na aikata miyagun laifuka su samu damar fasowa don yi musu fashi.
Har yanzu fim din a sinima kawai ake samunsa.
Ya kuma samu damar shiga sahun fina-finai don samun lambar yabo.
Ya samu karbuwa ne saboda irin sakon da yake isarwa, wanda gaba daya ya sha bamban da irin fina-finan Kannywood na soyayya.
Kuma ya dace da zamanin da ake ciki musamman yayin da kungiyar kwadago ke ta fama da gwamnati wajen ganin an samu karin albashi.

6. Mariya





Fim din MariyaHakkin mallakar hotoINSTAGRAM/ALI NUHU
Image captionFim din Mariya

Fim din Mariya, wanda Ali Nuhu ne daraktansa, yana nuni ne kan yadda lamarin auren 'ya mace yake a kasar Hausa.
Labari ne na Maryam Yahaya, wacce ta fito a matsayin Mariya kuma ake tuhumarta da kashe mijinta, Baba Karkuzu, da abokinsa, Musa Maisana'a, ta hanyar saka musu guba.
Kafin a yi mata auren dole, tare da Abdullahi (Umar M. Sharif) take soyayya.
Ga shi tana da buri na karantar aikin likita.
Daga bisani sai aka gano ashe ba ita ta yi kisan ba.
Babban kuskure a cikin fim din shi ne rashin fito da takamammun al'amura fili.
Duk da haka, fim din ya dace da zamanin da ake ciki yanzu.
'Yan wasa ma sun yi kokari.
Maryam Yahaya, kamar yadda ta saba, ta yi abin a-zo-a-gani.
Wadanda suka fito hatsabibai ma kamar su Garzali Miko, Baba Kurzuku, da Alhassan Kwalle sun taka rawar gani.
Tacewa da haskakawa da kuma kwalliya a fim din suna da jan hankali.

7. Larai Ko Jummai





Maryam Yahaya da Amal Umar a fim din Larai ko JummaiHakkin mallakar hotoINSTAGRAM/SADIQ MAFIA
Image captionMaryam Yahaya da Amal Umar a fim din Larai ko Jummai

Rikici tsakanin kishiyoyi ba bakon maudu'i ba ne a Kannywood yayin da nuna fada kan 'ya'yayen kishiyoyin kuwa abu ne bako.
Jummai (Amal Umar) da Larai (Maryam Yahaya) 'yan uba ne.
Yayin da mahaifiyar Jummai (Ladidi Fagge) masifaffiya ce, ta Larai kuwa ba haka take ba: shiru-shiru ce.
Mijinsu (wato Bashir Nayaya) yana ta hakuri da su dai.
Kamar yadda ya saba faruwa a kauyuka, kawai sai 'ya'yan baffanunsu (Abdul M. Sharif da Garzali Miko) suka tsunduma cikin soyayya da wadannan 'ya'yan Bashir Nayayan.
Da yake Garzali attajiri ne saboda a birni yake aiki, Ladidi sai da ta yi kutun-kutun ya auri 'yarta.
Kwatsam sai abubuwa suka sauya: Abdul ya zo ya fi Garzali kudi bayan ya bi shi sun tafi birni tare.
Sadiq N. Mafia ne daraktan fim din kuma shi wannan fim ya kece sauran fina-finai saboda dalilai da dama, duk da bai watsu kamar sauran fina-finai ba saboda ba a kashe masa kudi sosai ba.
Fim ne da ke matukar nuna zahiri, wanda za mu iya cewa shi ne zakara wajen nuna ainihin rayuwar Hausawa a kauye da kuma rashin jituwa kan "abin da bai taka kara ya karya ba" da ke tsakanin kishiyoyi a gidan mijinsu.

8. Taqaddama





Fim din TakaddamaHakkin mallakar hotoINSTAGRAM/ALI GUMZAK
Image captionFim din Takaddama

Fim ne da Ali Gumzak ne daraktansa kuma labari ne na "abin da ya taba faruwa da gaske" na wani sangartaccen dan wani shahararren mai kudi, Hassanu (Aminu Sharif).
Duk lokacin da ya yi laifi aka kulle shi, attajirin mahaifinsa, Alhaji Bilya (Ali Nuhu), wanda yake kut-da-kut da 'yan siyasa, kan ba da kudi domin a sake shi.
Ga shi mahaifin ba ya karbar shawara ko uzurin kowa.
Sai dai Hassanu da mahaifin nasa karshensu bai yi kyau ba bayan ya kashe abokinsa, Salisu, a lokacin da suka yi rigima a wani gidan rawa.
Hassanu ya ja kunne wa dayan abokinsu, Nura (Abba Almustapha), wanda aka yi kisan a gabansa, cewa kar ya fada wa kowa shi ma zai kashe shi.
Sai dai Nura bai iya barin wannan barazana a zuciyarsa ba, wanda hakan shi ya tona asirin wanda ya yi kisar, wato Hassanu.
Fim din ya yi kokari wajen nuno yanayin rayuwar manyan Najeriya.
'Yan wasan sun yi kokari.
Shirin Ya koyar da darasi sosai, duk da cewa "kayatarwa" da "koyar da darasi" a lokaci guda abu ne da Kannywood ke fama da shi.

9. Kawayen Amarya





Fim din Kawayen AmaryaHakkin mallakar hotoINSTAGRAM/YAKUBU MOHAMMED
Image captionFim din Kawayen Amarya

Fim ne da 2 Effect Empire wanda kuma Yakubu Muhammad ya ba da umarni.
Kuma fim ne da 2 Effect din suka saba yin irinsa, wato mai kyale-kyale da kuma tattaro manyan taurari.
Labari ne na wani mai kudi, Alhaji Abdulsalam, da ke da mata uku.
Bai taba haihuwa ba.
Saboda fargabar haka sai ya dauko wani yaro ya mayar da shi a matsayin dansa.
Daga baya ma sai matan nasa suka samu juna biyu suka haihu.
Uwar gidansa (Saratu Gidado, wato Daso) kullum alfaharinta shi ne "ai mahaifinta ne sanadin kudin Alhaji", saboda haka, ya kamata komai nata da na danta ya zama daban.
'Ya'yan Alhaji (wato Ali Nuhu da Sani Danja da kuma Yakubu Muhammad) a rana guda suka yi aure.
Kamar yadda sunan fim din yake, haka fim din ma yake tattare da cakwakiya da kaceniya a yayi da bayan bikin auren, wanda yawancin kwayayen amaren ke janyowa.
Duk da fim din na ban-dariya ne, amma yana dauke da darrusa.
Babban matsalarsa ita ce "sautin ADR", wanda shi ne sake nadar murya don a saka wa fim kafin watsa shi.
Maganganun ba sa tafiya daidai da motsin lebe a fim din.
Haka dai babu abin da aka yi wa Daso bayan ta kashe mutane har biyu.
Fim ne da zai kayatar sosai.

10. Li'ani





Fim din Li'aniHakkin mallakar hotoINSTAGRAM/ALI GUMZAK
Image captionFim din Li'ani

Ali Gumzak ne daraktan wannan fim din.
Labari ne na wani mai suna Alhaji Sunusi (Rabiu Rikadawa), wanda sam ya ki yarda juna-biyun da matarsa ke da shi nasa ne.
Hakan ya kai ga sun je gaban alkali sun yi rantsuwa (Li'an).
Dan da ta haifa, wanda shi ne Ali Nuhu, a wajenta da mijin da ta aura ya girma.
Sai dai daga baya alhaki ya bi Alhaji Sunusi, wanda yake ganin kamar sakayya ce daga Ubangiji sakamakon abin da ya yi wa wannan matar tasa.
Mata takwas ya aura, yayin da daya daga cikinsu ta taba yunkurin kashe shi, amma hakan bai yiwu ba.
Sai da lokaci ya kure kafin ya gane kuskurensa.
Fim din ya hadu saboda irin maudu'in da ke ciki, wanda ba a saba yin fim a kansa ba.
Masu shirya fim din da 'yan wasan duk sun yi kokari sosai wajen saurin fito da al'amura fili.
Babu waka ko rawa a ciki.
Akwai wasu 'yan al'amura na daban wadanda su ma sun taimaka wajen isar da ainihin sakon fim din.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: BBC HAUSA