Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bayyana cewa za ta yi aiki da umurnin kotun daukaka kara dake zamanta a birnin tarayya Abuja da ta soke hukuncin babbar kotun tarayya da ta hana a saka yan takarar jam'iyyar APC a jihar Zamfara bisa gaza aiwatar da zaben fitar da gwani da hukumar zabe INEC ta bayar da adadin kwanakin kaidar da ya kamata a kammala shi.
A sanarwar da INEC din ya yi a shafinta na Twitter ta ce a yanzun yan takarar jam'iyyar APC tun daga matakin Gwamna da yan majalissar tarayya da kuma na jihohi za a kara da su a cikin zaben da za a fara gudanarwa daga gobe Asabar 23 ga watan February 2019
0 Comments:
Post a Comment