Saturday 8 December 2018




Wata sabuwa- atiku abubakar ya bayyana abinda gomnatinshi bazata amince dashiba inyaci zabe

Home Wata sabuwa- atiku abubakar ya bayyana abinda gomnatinshi bazata amince dashiba inyaci zabe

Anonymous

Ku Tura A Social Media

Dan takarar shugabancin kasa na jam'iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar ya yi alkawarin cewa ba zai bari wasu tsiraru su rika juya gwamnatinsa ba bayan ya yi nasara, hakan yasa ya yi alkawarin zai kafa gwamnatin hadaka da sauran jam'iyyun da suka goyi bayansa.

Alhaji Atiku Abubakar, dan takarar shugabancin kasa karkashin inuwar jam'iyyar PDP ya ce zai kafa gwamnatin hadaka bayan ya lashe zaben 2019 kuma ba zai amince wasu tsirarun azzalumai su rika juya akalar gwamnatinsa ba.

Ayiku ya yi wannan jawabin ne a ranar Juma'a a Abuja yayin da ya ke ganawa da hadakan jam'iyyun siyasan Najeriya CUPP da ke dauke da jam'iyyun siyasa 45 da suka goyi bayansa a matsayin dan takarar shugabancin kasarsu.

2019: Atiku ya fadi abinda gwamnatinsa ba za ta yarda da shi ba idan aka zabe shi

2019: Atiku ya fadi abinda gwamnatinsa ba za ta yarda da shi ba idan aka zabe shi

DUBA WANNAN: 2019: Ba za ayi adalci ba muddin Buhari bai amince da gyaran dokar zabe ba - SDP

Ya ce Najeriya na fuskantar kallubalen tsaro, tabarbarewar tattalin arziki da wasu matsalalolin.

Tsohon mataimakin shugaban Najeriyan ya ce ya shiga wannan takarar ne domin ya kawar da jam'iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki wadda ya ce ta gaza cikawa al'umma alkawuran da ta dauka yayin kamfen.

Share this


Author: verified_user

0 Comments: