Amurka za ta fallasa Iran
Amurka ta ce za ta gabatar da gyauron makamai waɗanda ta ce Iran ce ta samar wa ƴan-tawayen Huthi na Yemen.
Jakadiyar Amurka a majalisar ɗinkin duniya Nikkey Haley za ta nuna shaidar ga wakilan ƙasashen kwamitin sulhu na majalisar dinkin duniya, a ƙoƙarin da Amurka ke yi na ganin majalisar ɗinkin duniya ta ƙara takura wa Iran.
Watanni da dama ke nan tun bayan da ƙasar ta Amurka ke bibiyar majalisar ɗinkin duniya wajen ganin ta hukunta Iran, inda har Amurka ɗin ta yi barazanar ficewa daga yarjejeniyar jingine shirin makamin nukila da aka ƙulla da Iran.
Tuni dai Iran ta musanta cewa tana samar wa ƴan-tawayen Huthi makamai, sannan ta bayyana shirin Amurka ɗin a matsayin na bogi.
Sunday, 4 February 2018
Author: Anonymous verified_user
RELATED STORIES
List of Schools that offer Common law and Islamic Law under the Faculty of Law in Nigeria.Common law and Islamic Law - Faculty of Law.This
Lagos taci Ado Domin Bikin Kirsimeti click here👇🏻Duk shekara birnin Lagos na Najeriya na shan ado
NEWS: An Kama wani babban kamanda na Boko haram wanda ake nema danna kan hoton dan karantawa👇🏻Rundunar 'yan sandan Najeriya ta tabbatar da cewa
MTN Nigeria replies CBN on illegal repatriation of $8.1 billionMTN Nigeria on Thursday refuted the claims by the
NEWS:- Limaman Coci 700 Sunyiwa Dalibansu Fyade Limaman Coci 700 Sun Yi Wa KanananYara FyadeA na
Myschool CBT Challenge Season 5 - Cash Prize Of N200,000 To Be Won! We are pleased to announce the Myschool CBT Chall
0 Comments:
Post a Comment