Thursday, 8 November 2018




Karin albashi: 'Yan fansho na son a tuna da su

Home Karin albashi: 'Yan fansho na son a tuna da su

Anonymous

Ku Tura A Social Media
[post by samaila umar lameedo]

Karin albashi: 'Yan fansho na son a tuna da su

LABARAI DAGA 24BLOG
Latsa alamar lasifika a sama domin sauraren hirar Ibrahim Isa da shugaban 'yan fansho na Kano
'Yan Fansho a Najeriya sun bayyana cewa suna goyon bayan fafutukar da kungiyar kwadagon kasar ke yi ta neman naira dubu talatin a matsayin mafi karancin albashi domin karin da za a yi zai iya shafar rayuwarsu.
Ana dai dakon bangaren shugaban kasa ya yi nazarin yarjejeniyar da kungiyar kwadagon ta cimma da wani kwamitin gwamnati dangane da karin albashin naira 30,000 mafi kankanta.
Comrade Salisu Ahmed Gwale shi ne shugaban kungiyar `yan fansho na jihar Kano, kuma a tattaunawarsu da Ibrahim Isa ya ce su ma suna bukatar kari saboda abin da ake biyansu bai taka-kara-ya-karya ba.

Share this


Author: verified_user

0 Comments: