Shugaba Buhari yace kowa ya zabi wanda yake so
LABARAI DAGA 24BLOG
Shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari ya bayyana cewa yanzu kam 'yan Najeriya tuni suka waye domin kuwa lokacin murdiyar zabe, satar akwati da kuma anfani da hukumomin gwamnati don yin magudin zabe dukkan su sun wuce.
Haka zalika shugaban kasar ya kara da cewa yana shawartar 'yan Najeriya a ko'ina suke da su darje su zabi wanda ran su ke so a zabukan gama gari na shekarar 2019 masu zuwa a dukkan matakai.
Ba sauran sak: Shugaba Buhari yace kowa ya zabi wanda yake so
Shugaban kasar yayi wadannan kalaman ne lokacin da ya karbi bakincin wasu manyan jami'an majalisar dinkin duniya da kuma shugabannin kungiyar kasashen yammacin Afrika a ofishin sa dake Abuja.
Haka zalika shugaban kasar ya kuma bayar da tabbacin cewa gwamnatin sa zata yi dukkan iya kokarin ta wajen ganin zabukan na 2019 sun kasance sahihai a kowane irin ma'auni.
Friday, 2 November 2018
Author: Anonymous verified_user
RELATED STORIES
INEC ta sanar da lashe zaben shugaban kasa a Osun Buhari da Atiku su ne a gabaINEC ta sanar da lashe zaben shugaban kasa a Osun
Har ila yau, Hukumar INEC ta Kara daga zabe a Wadansu Yankuna.Har ila yau, Hukumar INEC ta Kara daga zabe a Wad
Gudun Shari'ar Kasa a Kullum Kamar yadda Kotun Koli ta Tarayyar Tarayya ta ba da umurni ga sabon zabe a jihar Kano. Gudun Shari'ar Kasa a Kullum Kamar yadda Kotun Ko
Sakamakon Zaɓuɓɓuka: Dubi yadda Atiku yake Buhari tazara mai Girma. Sakamakon Zaɓuɓɓuka: Dubi yadda Atiku yake Buhari
Shugaban Farfesa na INEC, Malam Mahmood Yakubu Ya ƘaddaraShugaban Farfesa na INEC, Malam Mahmood Yakubu Ya
Duba Kalmomi 7 masu karfi da Atiku ya furta a lokacin da akayi taron PDP NEC a yauDuba Kalmomi 7 masu karfi da Atiku ya furta a lok
0 Comments:
Post a Comment