Wednesday 5 December 2018




Kotu ta umarci EFCC, SSS da ’Yan sanda su damke Diezani cikin kwanaki uku

Home Kotu ta umarci EFCC, SSS da ’Yan sanda su damke Diezani cikin kwanaki uku

Anonymous

Ku Tura A Social Media
Mai Shari’a Valentine Ashi ta Babbar Kotun Tarayya da ke Apo, Abuja, ta bai wa jami’an EFCC, SSS da ‘yan sanda kwanaki uku daga jiya Talata, 4 Ga Disamba, cewa su kamo tsohuwar ministar harkokin man fetur a zamanin gwamnatin Goodluck Jonathan, Diezani Alison-Makueke.


Wannan umarni ya zo ne bayan da lauyan EFCC, Msuur Denga, ya roki kotun ta bayar da iznin a kamo Diezani, ta hanyar bayar da takardar iznin a kamo wanda ake zargi, wato ‘arrest warrant’.

Ya ce ta haka ne kawai za a iya gurfanar da ita a gaban kotu ta amsa tuhumomin da ake yi mata.

EFCC ta ce tun a ranar 3 Ga Oktoba, 2013 wata kungiyar kishin hana cin hanci main suna CACOL, ta kai rubutaccen korafi a kan Diezani cewa ta shiga cikin harkallar cuwa-cuwar makudan kudade a wasu ciniki da ta gudanar a madadin gwamnatin tarayya.

Ana zargin ta tare da tsohon shugaban kamfanin Atlantic Energy Drilling Company, Jide Omokore.

Sannan kuma ana tuhumar su da karbar kyautar wasu maka-makan gidaje birjik a Ikoyi, Lagos da Tsibirin Banana a Lagos.

Kotu ta nemi a kamo su a gurfanar da su a ranar 25 Ga Fabrairu, 2019.
Premiumtimeshausa.

Share this


Author: verified_user

0 Comments: