Showing posts with label Ra'ayi Riga. Show all posts
Showing posts with label Ra'ayi Riga. Show all posts

Wednesday, 2 January 2019

Karanta Kaji: Wa Za'a Yiwa Haka Idan ba Sayyadina Baba Buhari Ba Inji-Adam A. Zango

Karanta Kaji: Wa Za'a Yiwa Haka Idan ba Sayyadina Baba Buhari Ba Inji-Adam A. Zango

Fitaccen jarumin Masana'antar shirya fina-finan Hausa (Kannywood) Adam A. Zango ya wallafa wani saƙo a shafin sa na Instagram wanda ya ɗauki hankulan al'umma sosai.

Adam A. Zango tare da hotan taron da yayi furuci akai.


Wakilin Muryar Hausa24 ya yi duba ga wasu daga cikin  ra'ayoyin  mabiya shafin jarumin kamar haka:



Wannan shine abinda jarumin ya wallafa "WA ZA'A YIWA HAKA IDAN BA SAYYADINA BUHARI BA".

Ra'ayoyi....


Ra'ayoyi....


Ra'ayoyi....

Ra'ayoyi....

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: www.MuryarHausa24.com.ng

Friday, 23 November 2018

KARANTA KAJI: YADDA AKA FANSO 'YAN TAGWAYEN DA AKAYI GARKUWA DA SU A ZAMAFARA DA DARASIN DA ZAMU KOYA

KARANTA KAJI: YADDA AKA FANSO 'YAN TAGWAYEN DA AKAYI GARKUWA DA SU A ZAMAFARA DA DARASIN DA ZAMU KOYA

Lokacin da Maigirma Sanata Kabiru Marafa ya bada tallafinshi Naira miliyon shida da sauran kudin da jama'ar Nigeria suka tallafa aka hada kudin ya kai Naira miliyon goma sha biyar, sai aka kira wadanda sukayi garkuwa da tagwayen aka sanar musu cewa kudin ya cika kamar yadda sukace a biyasu kafin su saki tagwayen, bayan an sanar da su cewa kudin ya cika sai sukace to a jirasu zasu kira don a kai musu kudin.



Bayan kamar awa uku sai suka kira wayan Ibrahim mijin yayarsu wanda ake sasantawa da shi, sukace a dauko kudin azo wani gari da ake kira Gurbin-Burai inda kwanaki masu garkuwa da mutane sukayi kashe-kashe da kone-kone sukace idan an isa garin a kirasu, kafin su Ibrahim su isa garin masu garkuwa da tagwayen suna ta kiransu a waya cewa mai yasa har yanzu ba su iso ba? sun gaji da jira, su fa zasu kashe tagwayen suyi tafiyarsu sai dai azo a dauki gawarsu, Ibrahim dai yayi ta basu hakuri yana cewa mun kusan isowa.

Bayan su Ibrahim sun isa garin na Gurbin-Burai suka kira masu garkuwan aka fada musu cewa sun iso garin, sai sukace to daga nan su biyo ta wani kauye da ake kira Dumburum daga Dumburum daji za'a shiga, to su Ibrahim sai suka ajiye motarsu suka nemi mashina guda uku, sai masu garkuwan suka kira waya sukace ai mun ganku ko taho garin na Dumburum zamu fada muku hanyar da zakubi ta kawoku cikin jeji inda muke, jama'a kunga wannan ya nuna cewa akwai masu yiwa 'yan bindigar leken asiri ko ta ina a cikin wadannan garuruwa na Zamfara.

Daga garin Dumburum su Ibrahim sunyi tafiya kamar tsawon kilo mita 15 a cikin jeji, suna cikin tafiya kawai sai suka fara ganin mutane da bindigogi suna ta bullowa wanda yawansu ya kai kusan mutum dari da hamsin, kuma kowa rike yake da bindiga kirar AK47 ana cewa su dakata a gurin, sai su Ibrahim suka dakata suka sauka daga kan mashina, da ma su uku ne, da shi Ibrahim mijin yayarsu, da wanda zai auri Hussaina, da babban yayansu, sai Ibrahim ya dauko kudin ya ajiye a gabansa wanda aka zuba kudin a cikin jaka guda biyu, 'yan bindigar sun gewayesu a tsakiyar jeji, bayan kamar mintuna biyu sai ga shugaban kuma ogan 'yan bindigar ya bullo tare da tawagarsa rike da manyan bindigogi tagwayen suna bayanshi.

Haka shugaban barayin ya matso har kusa da Ibrahim inda kudin suke ajiye a cikin jaka a 'kasa, bai ce masa komai ba sai yayi umarni da wasu yaranshi guda biyu su bude jakan su kirga kudin, bayan sun kammala kirga kudin gaba daya ya cika miliyon 15, sai ogan yace a mayar da kudin cikin jaka a daure, da akayi haka, sai ogan barayin ya tsuguna a gaban kudin ya debi kasa da hannunshi ya watsa akan jakakkunan kudin, sai ya mike tsaye ya hau kan jakakkunan kudin da kafafunshi, sai ya daga kanshi sama yana karanta wasu 'dalasimai irin na tsafi, yana tayi har kusan kamar mintuna 2 sai ya saukar da kanshi kasa, ya kuma sauka daga jakar kudin ya ja da baya, sai yayi umarni ga yaranshi da su dauki kudin, sai suka dauka, sai ya kalli Ibrahim yayi dariya sai yace sannunku da zuwa ashe kuna son kannenku.

Sai Ibrahim ya amsa masa, sai yace ai ba wanda baya son kannenshi oga, daga nan sai yayi umarni da a kawo tagwayen ya mikasu ga Ibrahim yace su juya su tafi kar su kuskura su juya baya, Ibrahim yace mun gode oga, shine suka dauko tagwayen suka iso har kauyen Gurbin-Burai inda motarsu take, daga nan sai Ibrahim ya fara kiran waya suna sanar da 'yan uwa da wadanda suka tallafa cewa tagwayen sun kubuta lafiya.

Jama'a wannan shine bayanin abinda ya faru game da yadda akaje aka karbo tagwayen.

Abinda bincikenmu ya tabbatar mana shi ne an jima ana bibiyar tagwayen domin ayi garkuwa da su, mutane da dama suna da hannu a cikin garkuwa da 'yan matan, wato nazarin da mukayi a kai shine wadannan masu aikata laifin garkuwa da mutane sun kawo wata sabuwar hanyar yin garkuwa da mutane ta hanyar bibiyar mutanen da suke mu'amala da dandalin sada zumunta na zamani musamman wadanda suke watsa hotunansu a social media, masu garkuwan suna la'akari da farin jinin wanda yake social media da yawan jama'ar da suke tare da shi wanda idan sunyi garkuwa da shi dole za'a biyasu kudi.

Kunga wadannan tagwaye babban abinda yayi sanadiyyar jefa su cikin wannan bala'i shine saka hotunansu da suke yi a social media da irin yadda ake kambamasu, wadanda sukayi garkuwa da su sun dauki lokaci mai tsawo suna bin diddiginsu har zuwa ranar da tagwayen suka ziyarci garin Mahaifinsu domin su raba katin aurensu, garin kauye ne, a daren ranar da za'ayi garkuwa da su tun isarsu garin suke ta yawo, kuma duk inda suka wuce sai an nunasu, da dare yayi misalin karfe 11 da wasu mintuna akaje gidan kawarsu da suka sauka zasu kwana aka sacesu gaba daya, har da kanin mijin kawar tasu, da ita kawar tasu aka tafi dasu jeji.

Muna nazarin ayyukan masu garkuwa da mutane da dabarunsu, mun sani cewa idan masu garkuwa da mutane sun kama mutum biyu ko sama da haka, to ba sa yarda su sake daya ko biyu su bar wani, a'a sai dai su sakesu gaba daya, to amma wannan sun kamasu gaba daya, sai suka saki tagwayen sauran kuma ba'a sakesu ba, wannan zai tabbatar maka da cewa masu garkuwan sunyi karfin da ya wuce tunanin duk wani mai tunani ko hasashe da nazari, kuma wannan babban kalubale ne ga gwamnatin Nigeria, mahukunta sai sunyi da gaske imba haka ba masifar zata mamaye jihohi da dama a Nigeria.

Daga karshe ina kira ga 'yan mata da mazaje masu yada hotunansu a kafofin sada zumunta kuma suke da dunbin masoya da suyi taka tsantsan, sannan su kiyaye sirrin tsaron kawunansu, ku dena bayyana inda zakuje idan zakuyi tafiya, bayyanawan hatsari ne mai girma a irin wannan lokaci da muka tsinci kanmu, a dinga 6atar da kafa idan za'ayi tafiya ko za'a dawo daga tafiya.

Muna rokon Allah Ya tsaremu daga dukkan sharri da makirci da mugun tarko.

Yaa Allah duk masu bibiyarmu da sharri ko cutarwa Allah Ka mayar da sharrin da cutarwan zuwa kansu Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source:  Datti Assalafy



Sunday, 28 October 2018

KARANTA KAJI: JIHOHI GUDA BIYU A KASAR NIGERIA BAZASU TAƁA ZAUNAWA LAFIYA BA

KARANTA KAJI: JIHOHI GUDA BIYU A KASAR NIGERIA BAZASU TAƁA ZAUNAWA LAFIYA BA

Wadannan jahohi bazasu taba samun zaman lafiya ba har sai sun dawo ga tirbar da aka san su da ita.


1. JAHAR BORNO

2. JAHAR ZAMFARA.

Marubuci: Mansur Musa Mancy Wanzamai

Wadannan jahohi bazasu taba samun zaman lafiya ba har sai sun dawo ga tirbar da aka san su da ita.

jahar borno, duk Africa idan akazo fannin sanin ilimin qur'ani basuda na biu. Allah ya azurtasu da masana littafin sa mai tsalki amma sai suka maida qur'anin Allah abun yin sihiri da tsibbace-tsibbace, tare da amfani da ayoyin ubangiji ta mummunar hanya.

Shin kuna ganin Allah zai barsu haka, ba tare da ya jarabce su da ukubar sa ba !!!?

Haka kuma, Zamfara, Wadda akeyiwa kirari da "Noma da shari'a sune tunkahon mu," itace jaha ta farko a duk Africa data nunawa duniya cewa tayi alkawalin tafiyar da dukkanin lamurran ta abisa tsarin shariar musulunci.

Aka kafa shari'a, ko kuma ince aka jaddadata, amma daga bisani sai muka yaudari kawunan mu, mukayi watsi da shari'ar nan, harma munayiwa Allah izgikl, muka dauki kalamar "shari'a" wata kalma ta yaudarar al'umma.

Yau jahar zamfara takai matakin da duk wani kalar zunubi da aka aikatawa a Nigeria zamfara ta lunka shi.

Shin kuna ginin Allah zai kyale jahar zamfara ba tare da ya addabe mu da musibu kala-kala ba !!!?.

Ina mai rantsuwa da Allah akan cewa, wallahi Idan da zaa kawo dukkanin Africa a jahohin zamfara da borno bazasu iya kawar da wadannnan musibu da suka addabe mu ba har sai mun farfado daga barcin da mukeyi.

Gwamnati bazata iya kawo muna zaman lafiya ba, har sai mun dawo ga Allah.

Yazama dole ga malamai suyiwa gwamnati bore domin dawo da martabar Shari'a a jahar zamfara.

Yazama dole malaman Nigeria su yaki matsibbatan da suka addabi jahar borno idan har anson zaman lafiya ya wanzu a kasar mu Nigeria.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA ,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: www.MuryarHausa24.com.ng

Wednesday, 24 October 2018

Karanta Kaji: Wani Bawan Allah ya yiwa wanda ya kirkiri Tuwo da Miyan kuka Allah ya isa

Karanta Kaji: Wani Bawan Allah ya yiwa wanda ya kirkiri Tuwo da Miyan kuka Allah ya isa

Majiyar Mu ta Hutu dole ta bayyana mana Cewa"Wani bawan Allah ya yiwa wanda ya kirkiro Tuwo miyan Kuka Allah ya isa inda ya bayyana cewa ya cuce su."


Duk da Cewa"Mutumin bai bayyana dalilin sa ba, sai dai a ganin wakilin Muryar Hausa24 hakan ba dai-dai bane."


Wannan Ra'ayin Wakilin shafin  Muryar Hausa24 ne "Ko babu komai tuwo da miyan kuka ya gama maka komai a rayuwa amatasayin ka na bahaushe, ba kai ba harda iyayen ka, idan rai ya ɓaci bai kamata hankali ya gushe ba."

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA ,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: www.MuryarHausa24.com.ng


Sunday, 21 October 2018

Karanta Kaji: Manyan Aiyuka 3 da Buhari ya yi a Nigeria Waɗanda ba Kowa Bane Ya Sansu

Karanta Kaji: Manyan Aiyuka 3 da Buhari ya yi a Nigeria Waɗanda ba Kowa Bane Ya Sansu

Ba nufina ince ba'a samu gazawa a wasu bangarorin ba a zamanin mulkin Baba, tabbas nasan akwai al'amuran da wasu ke kalla a matsayin gazawa, amma dai yanzu ina son ne inyi magana akan wadannan abubuwan da aka samu nasara akansu.....



Marubuci: Rabiu Biyora

GASU.....

1.. Social Investment Programmes for Nigerian.

A kafin zuwan Gwamnatin Shugaba Buhari babu wannan tsarin gaba daya, amma yanzu an samu ikon tallafawa mutane sama da miliyan Goma kai tsaye ta cikin Tsarin, ga wasu dubunnan matasan da aka samawa aikin wucin gadi a N-Power ana basu N 30,000 duk karshen wata, ana bawa yara abunci a makaranta duk a cikin tsarin, Rance mara ruwa na N10,000 ga dubunnan mutanen Nigeria tare da sauran wasu ayyukan duk da akeyi a karkashin tsarin Social Investment wanda Shugaba Buhari ya samar....

2.. Rail Project......

Tun shekarar 1999 har zuwa 2015 babu Gwamnatin data iya kammala aikin shimfida titin jirgin kasa a Nigeria, amma cikin kasa da shekara Hudu na mulkin Shugaba Buhari yayi kokarin samar da manya manyan layukan jirgin kasa har guda uku tare da sabbin tashoshin jiragen kasa hadi da sabbin jiragen kasa, kunga ai yayi kokari ko.....

3... Rice Importation .....

A baya kasarmu ta kusan dogara ne gaba daya da shinkafar da ake shigowa da ita daga wasu kasashen Duniya, inda mu bama iya noma wacce zata iya ciyar damu, masana lissafi sun bayyana cewa ana shigo sa shinkafa sama da Ton Dubu dari shida a kowacce shekara, amma yanzu daga 2015 zuwa yau shinkafar da ake shigowa sa ita bata kai Ton Dubu Ishirin ba, wanda hakan ke nuna yanzu muna iya samar da shinkafar da muke bukata a kasarmu ba tare dasai mun dogara da kowacce kasa wajen cin abunci ba.....

Wadannan dana lissafa kadan ne daga cikin irin nasarorin da aka samu a zamanin mulkin Muhammadu Buhari, idan kenan muka kara zabarsa zuwa kankanin lokaci nasarar da kasarmu zata samu zasu kasance masu yawa, arziki zai kara yalwata a tsakaninmu.....

Kada kayi adawa cikin rashin gaskiya, idan har kaga kuskure ko karya a cikin abun dana rubuta zanso kayi bayanin dazai fito da gaskiyar karyar danayi maimakon ka karyatani kai tsaye, ka turan a Muryarhausa24@gmail.com .....

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA ,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: www.MuryarHausa24.com.ng

Thursday, 18 October 2018

Karanta Kaji: Manya Manyan Nasararorin da Mulkin Buhari Ya Samar a Arewacin Nigeria

Karanta Kaji: Manya Manyan Nasararorin da Mulkin Buhari Ya Samar a Arewacin Nigeria

'YAN UWA 'YAN AREWA MASU DARAJA DA ALBARKA, WAI SHIN ME YASA MUKE DA SAURIN MANTUWA HAR MUKA MANTA DA ABINDA GWAMNATIN PDP SUKA MANA?



Marubuci: Datti Assalafy

Har mun manta a lokacin gwamnatin PDP da aka tashi rugurguza garuruwanmu gaba daya aka tilasta wasu guduwa daga gidajensu zuwa sansanin 'yan gudun hijra?

Har mun manta lokacin da 'ya'yan wasunmu da kannenmu a makarantu ana dannesu a kasa ana yankawa kamar kaji, 'yan mata budurwai a zabi na zaba a gudu dasu a mayar dasu bayi ana saduwa dasu ala tilas ana musu fyade?

Ya dace mu manta da kisan da aka yiwa manyanmu na arewa 'yan mazan jiya irinsu General Shuwa, wasu manyanmu don dole suka tsere daga Kasar suka barmu a Nigeria ana kashe mana 'yan uwa ana ruguje mana gidaje da makarantu da kasuwanni?

Ba mu bane al'ummar da aka dinga hallaka mana manya manyan malaman musulunci, a bangaren darika aka hallaka malamin Allah salihi Sheikh Adam Misrah Nafada daga jihar Gombe, a bangaren izala aka kashe mana Almarhum Malam Auwal Albaniy Zaria da wasu manyan malamai, har akayi yunkurin hallaka mana sheikh Dahiru Usman Bauchi da Sheikh Sani Yahya Jingir da wasunsu, duk mun manta?

Ba mune jama'ar arewa da aka dinga shiga gidajenmu har cikin dakunan matanmu na aure ana 'daga mana karkashin gado na raya sunnar Manzon Allah (saw) da zummar wai ana binciken kayan ta'addanci, da zaran an samu ko da gwangwanin maltina ne sai a kama mutum ace wai na hada bomb ne, yanzu har mun manta da wannan wulakanci da aka mana a gwamnatin PDP?

Ba mu bane a arewa duk wasu hazikai jarumai da suka san sirrin kwangilar ta'addancin da aka kawo don a rusamu, hazikannan suka fara tona musu asiri irinsu Malam Ja'afar Kano, Malam Albaniy Zaria da wadanda suka dinga bada shawara akan hanyoyin da za'a kawo karshen ta'addancin sai da akaci amanarsu aka kamasu aka musu sharri wasu ma aka hallakasu duk don a jaddada ayyukan ta'addanci a yankinmu na arewa, yanzu duk mun manta da wannan?

'Yan uwa musulmin arewa har mun manta da lokacin da akayi yunkurin jawo dokar hana iyayenmu mata yawo da hijabi da nikabi sai dai su fita tsirara kamar matan maguzawa arna, idan akaga musulma da hijabi sai an tilastata ta cire an taba ko'ina a jikinta an shafa wai ana laluben bomb, saboda iskanci da iye shege, yanzu duk mun manta da wannan abinda akayi mana a gwamnatin PDP?

Kai 'dan arewa musulmi da kake kalubalantar shugaba Buhari kake zaginsa, shin an ta6a yiwa mahaifiyarka ko matarka irin wannan cin mutunci da wulakanci da keta haddi? tsakani da Allah idan an taba yiwa naka haka zaka 'kara kaunar jam'iyyar PDP?

Ba mune jama'ar da aka katangewa hanyoyi saboda checkpoints tafiyar awa daya ta koma awa biyar ko shida saboda tsananin bincike da bata lokaci, idan ka dauko mahaifiyarka a mashin bata da lafiya zaka kaita asibiti dole sai ta sauka ta taka da kafa wai kar ko kuna dauke da bomb, duk inda akaga mutum da gemu kawai anga 'dan ta'adda saboda rashin mutunci da makircin arna makiya addinin Allah, garuruwanmu sun koma kamar wadanda aka cinyesu da yaki sun koma kufayi, yanzu har mun manta da irin wannan kuncin rayuwa zamu sake komawa ga jam'iyyar PDP?

'Yan uwa musulmi 'yan arewa masu albarka har mun manta da lokacin da ake ganin jirage masu saukar ungulu suna sauka a dazukan garuruwanmu suna jibge makamai kullun ace jirgi ya sauka a jeji amma ba'asan daga ina yake ba, a Maiduguri da Yobe har akayi lokacin da idan anga jirgi mai saukar ungulu ya sauka a jeji to wannan ranar sai wani bala'i ya faru, kunaji kuna gani kuma duk duniya ta gani a gwamnatin PDP aka kama jirgin shugaban kungiyar addininsu Pastor Ayo Oritsejafor shakare da muggan makaman yaki da miliyoyin daloli za'a shigo dasu Nigeria aka kama jirgin a Kasar Afirka ta Kudu, yanzu duk mun manta wannan zamu sake komawa garesu?

Tsakani da Allah a lokacin gwamnatin PDP da akace wai akwai saukin dalar amurka da arahan shinkafa, ya iya toshe mana wannan bala'in da ya afkowa arewa a lokacin?

Shin da a saka maka bomb ko a harbeka da bindigar harbo jirgin sama (AA) ya tarwatsa naman jikinka, ko ayi maka yankan rago amma a saukaka maka farashin dalar amurka da arahan shinkafa a hallakaka a kame 'ya'yanka mata ko kannenka mata a tafi dasu dazuka ana jima'i dasu, wanne yafi sauki da a barka ka rayu da tsadar dalar amurka? don wallahi yunwar ma babu ita sai dai ga rago.

Don haka 'yan arewa musumman musulmi muyiwa kawunanmu karatun ta nutsu jama'a, kar muyi saurin manta wannan cin amana da aka mana a gwamnatin PDP, kunga haka bai taba faruwa ba a jihar Abia, ko Anambra, Enugu da sauransu.

Allah Ka sa mu fahimta.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA ,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: www.MuryarHausa24.com.ng

KARANTA KAJI: WA YA ƊANAWA GANDUJE TARKO ?

KARANTA KAJI: WA YA ƊANAWA GANDUJE TARKO ?

Labari ya karade 'kasa, kafofin watsa laburu sun yi ca, Duniya kuma duk ta daukwa ana ta yamididi da zargin gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje OFR, Khadimul Islam ya karbe Dalar rashawa da cin hanci ya danna cikin aljihu da takardu cikin wasu faya-fayan bidiyo da aka yada.


Marubuci: Garba Tela Hadejia

Har zuwa yau, labarin na cigaba da karada Duniya, kuma al'umma daban-daban su na cigaba da bayyana ra'ayoyinsu mabambanta kan wannan al'amari, wasu na gaskata fayafayan bidiyon wasu kuwa na daukwarsa a matsayin sharri da 'kage domin a 'batawa gwamna Ganduje suna.
Sai dai kuma, a 'bangarenta, gwamnatin Jihar Kanon, ta ci alwahin shigar da 'kara Kotu kan zargin 'bata suna da da ta ke yi wa gidan jaridar na (Daily Nigerian) karkashim jagorancin mawallafin jaridar, Malam Jafar ja'afar.

Shi kuma a nasa 'bangaren, Jafar Jafar, ya kafe 'kyam ya yi tsayuwar daka cikin 'karfin gwiwar yarda da sahihancin labarinsa tun ma kafin ya yada.

Ita kuma majalissar dokokin Jihar Kano, har ta yi azamar kafa kwamitin bincike domin nemo gaskiyar al'amari.

A gefe guda kuwa wasu daga cikin jami'ai da hadiman gwamnatin Kano, gami da wasu daga cikin masu sana'ar shirya fina-finai suna cigaba da ba wa gwamna Ganduje kariya.

A dan nazarin da na yi kan wannan batu, ko shakka babu wannan al'amari a iya cewa zai zame wani gagarumin 'kalubale ko wata gagarumar sarkakiya ko tsaka mai wuya ga wasu 'bangarori kamar haka:

1. Idan har ta tabbata wannan faifan bidiyo kirkirarsa aka yi, to ba shakka, an 'batawa gwamna Gwanduje suna kuma kamfanin jaridar zai iya fuskantar hukunci biyan tara ladan 'bata suna. Kuma daraja da kimar mawallafin da na gidan Jaridar ya zuba a idon Duniya. Kana jama'a za su daina gamsuwa da sahihancin labarinsu.

2. In ko ta tabbata gaske ne, to ba makawa kallo zai iya komawa sama, mutane za su maida hankali kacocan kan fadar shugaban 'kasa (Alhaji Muhammadu Buhari) mai rajin yaki da rashawa gami da jam'iyyar (APC) mai ikirarin kawo sauyi domin ji da ganin irin matakin da za su daukwa akai.

Idan ko suka nuna halin ko'inkula, ko suka 'dauki mataki na sako-sako, to daraja da kimar gwamnati kan yaki da rashawa za su ragu a idon al'umma da ma Duniya. In kuwa suka dauki matakin azo a gani to ba shakka martaba da kimar gwamnatin za ta sake 'karuwa, sannan 'yan 'kasa da Duniya gaba 'daya za su sake samun nutsuwa da yarda da ikirarin da gwamnatin take yi kan yaki da cin hanci da rashawa ba sani ba sabo.

3. Sannan idan har ta tabbata gaskiyar kuma hukunci mai tsanani ya biyo ta kan gwamna Ganduje, to ba shakka, za a iya danganta wannan al'amari da "rana dubu ta 'barawo, daya tak ta me kaya". Ma'ana ya jima yana karba rana daya ta fashe. Ko kuma a iya cewa "Gadar Zare Gwamna Ganduje ya taka", ko kuma wani danannen tarko aka dana masa ya bi ta kai. Ma'ana wadanda suka shirya al'amarin ba da na goron tare da nadar faifan bidiyon sun san yana da halin cin hanci da rashawar, ko kuma ba halinsa ba ne amma sun rude shi da daloli ya fada, su a karan kansu ko wasu makiya Gandujen ne suka hada baki da su wajen shirya masa wannan gada, kan wata manufa tasu ta daban ko kuma da nufin su yi amfani da ita a daidai wannan lokaci na kakar zabe, shi kuma ya taka, take kuma neman yin tafiyar ruwa da shi.

Abin jira a gani dai shi ne, samun sahihin bayanai kan ingancin faifan bidiyon daga masana kuma kwararru a fannin gami da binciken majalissa da na sassan tsaro, da kuma irin wainar da za a toya idan an kara a kotu da kuma bayan bayyanar sahihanci ko akasin haka na faifan bidiyon.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA ,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: www.MuryarHausa24.com.ng