Everton tana aiki tare da hukumar da take
yaki da nuna wariyar bambanci launin fata, don bincikar
wadanda suka rera waka ta wariyar launi ga dan wasanta dan
kasar Colombian Yerry Mina.
Kungiyar ta Everton tace tana da masaniyar cewa, an wallafa
faifayen Bidiyo na nuna banbanci launi, a shafin sada
zumunta na yanar gizon wasu wanda ta nisanta kanta da
cewar bata da alaka da kulob din.
A shekara ta 2017 an gargadi magoya bayan Manchester
United kan irin wannan munmunar dabi'ar ta wariyar launi fata
kan dan wasanta Romelu Lukaku.
Da zaran an kammala bincike wajan gano waddanda suka
aikata wannan lamari, hukumar ta yaki da nuna wariya zata
tura da rahoto zuwa ga hukumar kula da wasan kwallon kafa
ta Football Association domin hukunta wanda suke da hanu
kan lamarin.
0 Comments:
Post a Comment